fidelitybank

Nan da watan Maris zamu kammala tashar shigo da kaya a Kano – Bawuro

Date:

Shugaban tashar sauke kayayyaykin da ake shigo da su tsandauri ta Dala Inland Dry Port, Abubakar Bawuro, ya ce, kasuwanci tsakanin Najeriya da makwabciyarta ta Arewa, Jamhuriyar Nijar za ta samu ci gaba mai tarin yawa yayin da ake sa ran kaddamar da tashar a jihar Kano cikin watan Maris na 2022.

Ya ce, aikin wanda kawo yanzu ya lakume sama da Naira biliyan 5 na gine-gine ya kai sama da kashi 80 bisa 100 da aka kammala, tare da sauran ayyukan da ake sa ran za a yi nan da karshen watan Fabrairu na shirye-shiryen fara tashi.

Ya yin tattaunawa da magana labarai, a lokacin da ya ziyarci Sakataren zartarwa na Hukumar Kula da Jiragen Ruwa ta Najeriya (NSC), Mista Emmanuel Jime a Abuja.

A cewar Bawuro, “Muhimman wuraren ginin da suka hada da wurin da aka tara kwantenan tashohin ruwa a dakunan ajiyar kaya da guraben aikin gudanarwa da hanyoyin shiga da kuma samar da wutar lantarki a tashar, an yi su sosai. Idan ka duba su a ka tantance su gaba daya, za mu iya aminta da cewa mun kai sama da kashi 80 cikin 100 na kammalawa.

“Muna so mu tabbatar muku da cewa za mu yi aiki cikin awanni 24 a mako guda, domin ganin mun cimma burin ganin mun tabbatar da kuma kaddamar da tashar a karshen watan Maris”. In ji Bawuro.

Shugaban Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ruwa ta Najeriya, Mista Emmanuel Jime, ya yi alkawarin bayar da duk wani goyon bayan da ya dace, domin tabbatar da nasarar IDP na Dala.

 

sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuÉ—a

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiÉ—a wa Isra'ila wasu...

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naÉ—in...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa Æ´an wasan...
X whatsapp