fidelitybank

Nan da watan Maris zamu kammala tashar shigo da kaya a Kano – Bawuro

Date:

Shugaban tashar sauke kayayyaykin da ake shigo da su tsandauri ta Dala Inland Dry Port, Abubakar Bawuro, ya ce, kasuwanci tsakanin Najeriya da makwabciyarta ta Arewa, Jamhuriyar Nijar za ta samu ci gaba mai tarin yawa yayin da ake sa ran kaddamar da tashar a jihar Kano cikin watan Maris na 2022.

Ya ce, aikin wanda kawo yanzu ya lakume sama da Naira biliyan 5 na gine-gine ya kai sama da kashi 80 bisa 100 da aka kammala, tare da sauran ayyukan da ake sa ran za a yi nan da karshen watan Fabrairu na shirye-shiryen fara tashi.

Ya yin tattaunawa da magana labarai, a lokacin da ya ziyarci Sakataren zartarwa na Hukumar Kula da Jiragen Ruwa ta Najeriya (NSC), Mista Emmanuel Jime a Abuja.

A cewar Bawuro, “Muhimman wuraren ginin da suka hada da wurin da aka tara kwantenan tashohin ruwa a dakunan ajiyar kaya da guraben aikin gudanarwa da hanyoyin shiga da kuma samar da wutar lantarki a tashar, an yi su sosai. Idan ka duba su a ka tantance su gaba daya, za mu iya aminta da cewa mun kai sama da kashi 80 cikin 100 na kammalawa.

“Muna so mu tabbatar muku da cewa za mu yi aiki cikin awanni 24 a mako guda, domin ganin mun cimma burin ganin mun tabbatar da kuma kaddamar da tashar a karshen watan Maris”. In ji Bawuro.

Shugaban Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ruwa ta Najeriya, Mista Emmanuel Jime, ya yi alkawarin bayar da duk wani goyon bayan da ya dace, domin tabbatar da nasarar IDP na Dala.

 

labaran duniya na yau

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaÉ—an wajen tsaron Æ™asa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haÉ—in...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar Æ´an Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaÉ“e shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...
X whatsapp