Shugaban tashar sauke kayayyaykin da ake shigo da su tsandauri ta Dala Inland Dry Port, Abubakar Bawuro, ya ce, kasuwanci tsakanin Najeriya da makwabciyarta ta Arewa, Jamhuriyar Nijar za ta samu ci gaba mai tarin yawa yayin da ake sa ran kaddamar da tashar a jihar Kano cikin watan Maris na 2022.
Ya ce, aikin wanda kawo yanzu ya lakume sama da Naira biliyan 5 na gine-gine ya kai sama da kashi 80 bisa 100 da aka kammala, tare da sauran ayyukan da ake sa ran za a yi nan da karshen watan Fabrairu na shirye-shiryen fara tashi.
Ya yin tattaunawa da magana labarai, a lokacin da ya ziyarci Sakataren zartarwa na Hukumar Kula da Jiragen Ruwa ta Najeriya (NSC), Mista Emmanuel Jime a Abuja.
A cewar Bawuro, “Muhimman wuraren ginin da suka hada da wurin da aka tara kwantenan tashohin ruwa a dakunan ajiyar kaya da guraben aikin gudanarwa da hanyoyin shiga da kuma samar da wutar lantarki a tashar, an yi su sosai. Idan ka duba su a ka tantance su gaba daya, za mu iya aminta da cewa mun kai sama da kashi 80 cikin 100 na kammalawa.
“Muna so mu tabbatar muku da cewa za mu yi aiki cikin awanni 24 a mako guda, domin ganin mun cimma burin ganin mun tabbatar da kuma kaddamar da tashar a karshen watan Maris”. In ji Bawuro.
Shugaban Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Ruwa ta Najeriya, Mista Emmanuel Jime, ya yi alkawarin bayar da duk wani goyon bayan da ya dace, domin tabbatar da nasarar IDP na Dala.