fidelitybank

Nakasassu 500 za su ci gajiyar inshorar lafiya – Gwamnati

Date:

Gwamnatin tarayya ta ce, ta shigar da nakasassu 500 cikin shirin inshorar lafiya na kasa (NHIS), domin inganta hanyoyin samun ingantattun ayyukan kiwon lafiya.

Babban sakataren ma’aikatar jin kai da ci gaban jama’a, Dakta Sani Gwarzo, ne ya bayyana hakan a wani taron ba da katin cin gajiyar shirin inshorar lafiya ga waɗanda suka amfana a Abuja.

A cewarsa, matakin zai tabbatar da samar da ayyukan kula da lafiya cikin sauki ga masu buƙata ta musamman a fadin kasar.

Gwarzo ya yi wannan jawabi ne a lokacin da ya jagoranci jami’an ma’aikatar lafiya zuwa fadar sarkin Karo Majiji kuma shugaban masu buƙata ta musamman a Abuja.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ta ruwaito cewa hukumar kulla da masu buƙata ta musamman ta ƙasa (NCPWD) ce ta dauki nauyin yin rijistar.

An dauki matakin ne domin rage wahalhalun da mutane masu nakasa ke fuskanta wajen samun ayyukan kula da lafiya.

Ya ce gwamnati ta fara aiwatar da shirin ne a babban birnin tarayya kuma ana sa ran za a faɗaɗa shi zuwa jihohi 36 na Najeirya.

vanguard newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp