Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin kwashe ƴan ƙasarta da suka maƙale a ƙasashen Isra’ila da Iran, bayan tsanantar rikici tsakanin ƙasashen biyu.
A cikin wata sanarwa da aka fitar a daren Talata, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin waje, Kimiebi Ebienfa, ya ce jakadun Najeriya a Tel Aviv da Tehran na ci gaba da tuntuɓar ’yan ƙasar da rikicin ya rutsa da su, tare da aikin tabbatar da cewa an kwashe su cikin aminci da kariya.
Ma’aikatar ta buƙaci ’yan Najeriya da ke zaune a Isra’ila da Iran da su bi dukkan matakan tsaro da hukumomin ƙasashen suka shimfiɗa, sannan kuma su hanzarta tuntuɓar ofishin jakadancin Najeriya mafi kusa domin yin rajista da samun ƙarin shawarwari.
Ma’aikatar ta yaba wa jajircewar ofisoshin jakadancin Najeriya a Isra’ila da Iran wajen tuntuɓar ’yan ƙasar a wannan lokaci mai cike da ƙalubale, tare da jaddada cewa kariyar lafiyar ’yan Najeriya da ke kasashen waje na daga cikin manyan abubuwan da gwamnati ke bai wa muhimmanci.
“Ma’aikatar harkokin waje na sanar da cewa sakamakon rikicin da ke ƙara tsananta tsakanin Isra’ila da Iran, Gwamnatin tarayya na kammala shirye-shiryen kwashe ’yan Najeriya da ke cikin mawuyacin hali a ƙasashen biyu.” in ji sanarwar.
Sanarwar ta zo ne bayan hare-haren sama da Isra’ila ta kai a ranar Juma’a, inda ta hari wurare kimanin 100 a fadin Iran, ciki har da cibiyoyin nukiliya da na soji inda hare-haren suka hallaka manyan jami’an sojin Iran da dama.