fidelitybank

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Date:

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin kwashe ƴan ƙasarta da suka maƙale a ƙasashen Isra’ila da Iran, bayan tsanantar rikici tsakanin ƙasashen biyu.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a daren Talata, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin waje, Kimiebi Ebienfa, ya ce jakadun Najeriya a Tel Aviv da Tehran na ci gaba da tuntuɓar ’yan ƙasar da rikicin ya rutsa da su, tare da aikin tabbatar da cewa an kwashe su cikin aminci da kariya.

Ma’aikatar ta buƙaci ’yan Najeriya da ke zaune a Isra’ila da Iran da su bi dukkan matakan tsaro da hukumomin ƙasashen suka shimfiɗa, sannan kuma su hanzarta tuntuɓar ofishin jakadancin Najeriya mafi kusa domin yin rajista da samun ƙarin shawarwari.

Ma’aikatar ta yaba wa jajircewar ofisoshin jakadancin Najeriya a Isra’ila da Iran wajen tuntuɓar ’yan ƙasar a wannan lokaci mai cike da ƙalubale, tare da jaddada cewa kariyar lafiyar ’yan Najeriya da ke kasashen waje na daga cikin manyan abubuwan da gwamnati ke bai wa muhimmanci.

“Ma’aikatar harkokin waje na sanar da cewa sakamakon rikicin da ke ƙara tsananta tsakanin Isra’ila da Iran, Gwamnatin tarayya na kammala shirye-shiryen kwashe ’yan Najeriya da ke cikin mawuyacin hali a ƙasashen biyu.” in ji sanarwar.

Sanarwar ta zo ne bayan hare-haren sama da Isra’ila ta kai a ranar Juma’a, inda ta hari wurare kimanin 100 a fadin Iran, ciki har da cibiyoyin nukiliya da na soji inda hare-haren suka hallaka manyan jami’an sojin Iran da dama.

vgn news 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Najeriya na cece-kuce dangane da rasuwar Muhammadu Buhari

Mutuwar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ta bar cece-kuce ga...

Da Ɗumi-Ɗumi: Kashim Shettima zai rako gawar Muhammadu Buhari zuwa Najeriya

Tsohon Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya rasu. Ya rasu ne...

Ina Tinubu ya ke ya ɓata ba bayani – ADC

Jam'iyyar African Democratic Congress wato ADC, ta soki Shugaba,...

Koriya ta Arewa za ta ba Rasha ƙarin sojoji domin yaƙin Ukraine

Shugaban Koriya ta Arewa Kim Jong Un ya yi...

Jam’iyyar ADC alheri ce ga siyasar Najeriya – Femi Gbajabiamila

Shugaban ma'aikata na fadar gwamnatin Najeriya, Femi Gbajabiamila ya...

Tinubu na yunkurin tauye hakkin ma’aikata – Atiku

Tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a Najeriya, Atiku Abubakar, ya...

Trump ya lafta wa ƙasashen Tarayyar Turai da Mexico harajin kashi 30

Shugaban Amurka Donald Trump ya lafta wa ƙasashen ƙungiyar...

INEC ta ce za ta buɗe shafin intanet domin rajistar sababbin jam’iyyu

Huhukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC, ta ce nan...

EFCC na neman Rabi’u Auwalu Tijjani ruwa a jallo a Kano

Hukumar da ke yaki da masu yi wa tattalin...

An gano musabbabin hatsarin jirgin saman Indiya

Masu bincike sun bayyana sakamako na farko-farko game da...

Amurka ta haramta wa shugaban kasar Cuba shiga kasar

Amurka a karon farko ta ƙaƙaba takunkumi kan shugaban...

An kashe mutum 6,800 tare da sace 5,402 a 2025 Najeriya – Rahoto

Alƙaluma na nuna cewa an kashe mutum dubu shida...
X whatsapp