fidelitybank

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Date:

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin kwashe ƴan ƙasarta da suka maƙale a ƙasashen Isra’ila da Iran, bayan tsanantar rikici tsakanin ƙasashen biyu.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a daren Talata, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin waje, Kimiebi Ebienfa, ya ce jakadun Najeriya a Tel Aviv da Tehran na ci gaba da tuntuɓar ’yan ƙasar da rikicin ya rutsa da su, tare da aikin tabbatar da cewa an kwashe su cikin aminci da kariya.

Ma’aikatar ta buƙaci ’yan Najeriya da ke zaune a Isra’ila da Iran da su bi dukkan matakan tsaro da hukumomin ƙasashen suka shimfiɗa, sannan kuma su hanzarta tuntuɓar ofishin jakadancin Najeriya mafi kusa domin yin rajista da samun ƙarin shawarwari.

Ma’aikatar ta yaba wa jajircewar ofisoshin jakadancin Najeriya a Isra’ila da Iran wajen tuntuɓar ’yan ƙasar a wannan lokaci mai cike da ƙalubale, tare da jaddada cewa kariyar lafiyar ’yan Najeriya da ke kasashen waje na daga cikin manyan abubuwan da gwamnati ke bai wa muhimmanci.

“Ma’aikatar harkokin waje na sanar da cewa sakamakon rikicin da ke ƙara tsananta tsakanin Isra’ila da Iran, Gwamnatin tarayya na kammala shirye-shiryen kwashe ’yan Najeriya da ke cikin mawuyacin hali a ƙasashen biyu.” in ji sanarwar.

Sanarwar ta zo ne bayan hare-haren sama da Isra’ila ta kai a ranar Juma’a, inda ta hari wurare kimanin 100 a fadin Iran, ciki har da cibiyoyin nukiliya da na soji inda hare-haren suka hallaka manyan jami’an sojin Iran da dama.

network news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp