Najeriya ta karɓi allurar rigakafin korona miliyan ɗaya samfurin Johnson and Johnson daga ƙasar Girka.
Ministan Harkokin Waje na Girka Nikolaos Dendias ne ya bayyana hakan ranar Litinin yayin wata ganawa da jami’an gwamnatin Najeriya a Abuja.
Ya ce sun ba wa Najeriya sadakar allurar ce da zimmar ƙarfafa mata gwiwa kan aikin kare mutane daga annobar.
Gwamnatin Najeriya na ƙara ƙaimi wajen ganin an yi wa ‘yan ƙasar masu yawa rigakafin na korona, inda har aka fara jaddada wa wasu a karo na uku sakamakon fargabar yaɗuwar nau’in Omicron na cutar.
Najeriya ta lalata rigakafi kusan miliyan ɗaya a watan Disamba bayan sun lalace, abin da ya sa ta yi alwashin cewa ba za ta sake karɓar alluran da suka kusa lalacewa ba.