Fitacciyar jarumar fina-finan Hausa, Nafisa Abdullahi ta ce ba za ta ci gaba da fitowa a cikin shiri mai dogon zango na Labarina ba.
Nafisa Abdullahi, wacce ke fitowa a matsayin SUmayya a cikin shirin, ta baiyana hakan cikin wata wasiƙa da ta aikewa mashiryin shirin, Aminu Saira ranar Asabar.
Jarumar ta ce ba za ta ci gaba da fitowa a cikin shirin ba sakamakon ƙarancin lokacin da ta ke da shi cikin al’amuran rayuwarta.
“Na fita daga cikin shirin ne saboda yadda al’amura suka yi min yawa, da hakan na tabbatar ba zai bani damar ci gaba da fitowa a shirin ba.
“Na ji dadin kasancewa cikin shirin LABARINA kwarai da gaske, kuma na yi mua’ala mai kyau da dukkanin abokannan aiki na na cikin shirin, tun daga kan mashiryin shirin har zuwa abokan aiki.
Jarumar tace tana son ta maida hankali kan kasuwancinta dakuma kamfaninta, harma da shirin fim da takeyi na kashin kanta.