Shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan ya isa jihar Katsina, a safiyar ranar Asabar, domin halartar bikin nadin sarautar Yusuf dan shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Gwamnan jihar Katsina, Aminu Bello Masari ne ya tarbe shi a filin jirgin Umaru Musa Yar’adua da ke Katsina.
Sarkin Daura, Alhaji Umar Farouk, zai nada Yusuf rawani a matsayin Talban Daura, wanda zai zama Hakimin Kwasarawa.
An shirya gudanar da taron ne a Daura, mahaifar shugaba Buhari.
A tare da Shugaban Majalisar Dattawa daga Abuja akwai Sanata Yusuf Abubakar Yusuf da Mohammed Sani Musa da kuma Bello Mandiya.
A na sa ran shugaban majalisar dattawan ya dawo Abuja nan take bayan kammala taron.
A lokacin da ya nada sabbin hakimai guda hudu a ranar Alhamis, Sarkin Daura ya ce, sun yanke shawarar yi wa dan Buhari rawani ne domin hana sabon Talba yawo daga Abuja da Yola, mahaifar mahaifiyarsa, lokacin da wa’adin shugaban ya kare.
Shugaban kasa Muhammadu Buhari tar da mai dakin sa, Aisha Buhari na kasar Turkiyya, domin halartar wasu ayyuka.