fidelitybank

Na yi takaici da na yi musabaha da shugaban Isra’ila – Erdogan

Date:

Shugaban ƙasar Turkiyya Recep Tayyip Erdogan, ya yi kakkausar suka kan matakin da gwamnatocin ƙasashen Yamma suka ɗauka kan hare-haren da Isra’ila ke kai wa Gaza,

Mista Erdogan ya ce ƙasashen Yamma sun kasa ɗaukar matakan da suka dace don magance rikicin saboda jinin musulmai ake zubarwa.

Shugaban na Turkiya ya nuna shakku kan yadda ake aiwatar da yarjejeniyar kare haƙin bil-Adama ta duniya, yana mai cewa da alama ƙasashen yammacin duniya kan yi watsi da ita, idan ba ta dace da muradunsu ba, musamman idan ya shafi asarar rayukan musulmai.

A wani muhimmin mataki, Erdogan ya soke ziyarar da ya shirya zuwa Isra’ila tare da nuna nadamar yin musabaha da firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu a taron Majalisar Dinkin Duniya da aka yi a birnin New York a watan da ya gabata.

Wannan yana nuna gagarumin sauyi a dangantakar diflomasiyyar ƙasashen biyu.

A halin da ake ciki kuma, ministan harkokin wajen gwamnatin Falasɗinawa, Riyad al-Maliki, wanda ke kula da Gaɓar Yamma da ƙogin Jordan, ba Gaza ba, ya bayyana hare-haren da Isra’ila ta kai a matsayin “yakin ɗaukar fansa.”

Da yake jawabi a kotun hukunta manyan laifuka ta ƙasashen duniya da ke kasar Netherlands, al-Maliki ya jaddada cewa harin boma-bomai a Gaza na baya-bayan nan ya fi tsanani fiye da hare-haren da Isra’ila ta kai a baya, ya kuma yi kira a gaggauta tsagaita wuta.

legit new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp