fidelitybank

Na girgiza da kisan Nabeeha a hannun ‘yan bindiga – Matar Tinubu

Date:

Mai ɗakin shugaban shugaba Tinubu Sanata Oluremi Tinubu ta bayyana kaɗuwarta kan mutuwar Nabeeha Al-Kadriyar, da ƴan bindiga suka halaka.

A wani saƙo da ta wallafa a shafinta na X, Sanata Oluremi ta bayyana mutuwar Nabeeha a matsayin rashi mai matuƙar sosa zuciya inda kuma ta miƙa ta’aziyyarta ga iyalan marigayiyar.

Sanata Oluremi ta kuma buƙaci ƴan Najeriya su haɗa kansu wajen yin addu’oi da za su kai ga sakin ƴan’uwan Nabeeha, waɗanda har yanzu ke a hannun masu garkuwa.

Da take magana kan ƙaruwar matsalar tsaro da sace-sacen jama’a, Oluremi ta yi kira ga hukumomin tsaro su ƙara ƙaimi wajen hana satar jama’a su kuma yi duk mai yiwuwa domin kuɓutar da ƴan’uwan Nabeeha.

A ranar 2 ga watan Janairu Nabeeha da ƴan’uwanta suka faɗa hannun ƴan bindiga a yankin Bwari da ke Abuja, babban birnin Najeriya.

Mahaifinsu Mansoor Al-Kadriyar, wanda shi ma ya shiga hannun masu garkuwar daga bisani sun sake shi domin ya dawo gida a haɗa kuɗin fansar ƴaƴansa.

Sai dai masu garkuwa sun ƙara kuɗin fansar tare da kashe Nabeeha bayan da aka gaza haɗa kuɗin fansar.

Sun kuma yi barazanar kashe ragowar ƴan matan da ke hannunsu idan aka ƙi biyan su kuɗi kafin wa’adin da suka ɗiba.

ng news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp