fidelitybank

Mutuwar Dr. Ahmad babban rashi ne ga al’ummar musulmai – Ganduje

Date:

Gwamna jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana rasuwar Dr Ahmad Muhammad Ibrahim Bamba, fitaccen malamai a cibiyar Darul Hadith da ke Kano, a matsayin babban rashi na jiga-jigan masu samar da zaman lafiya da kuma tarin ilimin Hadisi.

Dr. Ganduje ya sanar da hakan ne ta hannun babban sakataren yada labaran sa, Abba Anwar, wanda ya rabawa manema labarai.

Mutuwarsa ba karamin rashi a a ka yi wa jihar ba. Ya kara da cewa, marigayi malamin ya kasance hazikin malami, mai zurfin hazaka da asali, a cikin karantarwarsa na fadin manzon Allah Muhammadu tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.

“Ya kasance mai karfafa zaman lafiya tare a cikin lumana, wanda tsarin koyarwarsa ya kasance da nufin samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a tsakanin dukkanin bangarori da ma sauran su. Wannan babban rashi ne da ke tattare da bakin ciki da rashin maye gurbinsa,” in ji gwamnan.

Gwamna Ganduje ya bukaci malaman addinin Musulunci da su yi kokari tare da yin koyi da kyawawan halaye na marigayi Sheikh. Ya na mai jaddada cewa, “Ya kafa ginshikin yadda a ke yin Da’awa kuma ya bi abin da ya ke wa’azi. Mutum mai daraja ta kowane hali.”

Da ya ke ci gaba da cewa, “A madadin gwamnati da al’ummar jihar Kano, ina mika ta’aziyyarmu ga iyalan Sheikh Dr Ahmad Muhammad Ibrahim, ba wai iyalansa ba, Kano ko Nijeriya baki daya, duk al’ummar duniya baki daya sun yi asarar wani abu mai wuyar gaske.”

Ya roki Allah Madaukakin Sarki da ya gafarta masa dukkan kurakurensa, ya kuma saka masa da alherinsa da Jannatul Fiddaus.

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp