fidelitybank

Mutuwar Dr. Ahmad babban giɓi ne a duniyar ilimin Hadisi – Atiku

Date:

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya miƙa saƙon ta’aziyyar rasuwar babban malamin addinin nan na Kano, Sheikh Ahmad Muhammad Ibrahim Bamba, wanda a ka fi sani da Kala Haddasana wanda ya rasu a jiya Juma’a.

Atiku wanda ya wallafa sakon ta’aziyyar a shafinsa na Facebook a ranar Juma’a ya ce, ya yi matuƙar kaduwa lokacin da ya samu labarin rasuwar Dr. Ahmad.

“Na kaɗu matuƙa da samun labarin rasuwar Dr. Ahmad Ibrahim Bamba”.

“Rasuwar Shehin Malamin ya bar babban giɓi a duniyar ilimin Hadisi wanda zai yi wahalar cikewa.

“Mutuwar sa babban rashi ne ga duniyar Ilimin Hadith da sauran rassan Ilman Musulunci. Ya sadaukar da dukkan rayuwarsa wajen ilmantarwa da wayar da kan mutane. Haƙiƙa an saurari karatuttukansa a dukkan sassan duniya”.

“Ina addu’ar Allah ya ji ƙan sa sannan ya bai wa iyalai da abokansa haƙurin rashinsa. “Addu’ar Allah ya gafarta masa zunubansa, Ya haɗa shi da salihan bayi, ya kuma ba shi Aljannatul Firdaus. Ameen”. In ji Atiku

Sheikh Dr. Ahmad ya rasu ne bayan gajeriyar rashin lafiya a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...
X whatsapp