fidelitybank

Mutuwar Dr. Ahmad babban giɓi ne a duniyar ilimin Hadisi – Atiku

Date:

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya miƙa saƙon ta’aziyyar rasuwar babban malamin addinin nan na Kano, Sheikh Ahmad Muhammad Ibrahim Bamba, wanda a ka fi sani da Kala Haddasana wanda ya rasu a jiya Juma’a.

Atiku wanda ya wallafa sakon ta’aziyyar a shafinsa na Facebook a ranar Juma’a ya ce, ya yi matuƙar kaduwa lokacin da ya samu labarin rasuwar Dr. Ahmad.

“Na kaɗu matuƙa da samun labarin rasuwar Dr. Ahmad Ibrahim Bamba”.

“Rasuwar Shehin Malamin ya bar babban giɓi a duniyar ilimin Hadisi wanda zai yi wahalar cikewa.

“Mutuwar sa babban rashi ne ga duniyar Ilimin Hadith da sauran rassan Ilman Musulunci. Ya sadaukar da dukkan rayuwarsa wajen ilmantarwa da wayar da kan mutane. Haƙiƙa an saurari karatuttukansa a dukkan sassan duniya”.

“Ina addu’ar Allah ya ji ƙan sa sannan ya bai wa iyalai da abokansa haƙurin rashinsa. “Addu’ar Allah ya gafarta masa zunubansa, Ya haɗa shi da salihan bayi, ya kuma ba shi Aljannatul Firdaus. Ameen”. In ji Atiku

Sheikh Dr. Ahmad ya rasu ne bayan gajeriyar rashin lafiya a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp