fidelitybank

Mutuwar Dr. Ahmad babban giɓi ne a duniyar ilimin Hadisi – Atiku

Date:

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya miƙa saƙon ta’aziyyar rasuwar babban malamin addinin nan na Kano, Sheikh Ahmad Muhammad Ibrahim Bamba, wanda a ka fi sani da Kala Haddasana wanda ya rasu a jiya Juma’a.

Atiku wanda ya wallafa sakon ta’aziyyar a shafinsa na Facebook a ranar Juma’a ya ce, ya yi matuƙar kaduwa lokacin da ya samu labarin rasuwar Dr. Ahmad.

“Na kaɗu matuƙa da samun labarin rasuwar Dr. Ahmad Ibrahim Bamba”.

“Rasuwar Shehin Malamin ya bar babban giɓi a duniyar ilimin Hadisi wanda zai yi wahalar cikewa.

“Mutuwar sa babban rashi ne ga duniyar Ilimin Hadith da sauran rassan Ilman Musulunci. Ya sadaukar da dukkan rayuwarsa wajen ilmantarwa da wayar da kan mutane. Haƙiƙa an saurari karatuttukansa a dukkan sassan duniya”.

“Ina addu’ar Allah ya ji ƙan sa sannan ya bai wa iyalai da abokansa haƙurin rashinsa. “Addu’ar Allah ya gafarta masa zunubansa, Ya haɗa shi da salihan bayi, ya kuma ba shi Aljannatul Firdaus. Ameen”. In ji Atiku

Sheikh Dr. Ahmad ya rasu ne bayan gajeriyar rashin lafiya a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano.

network news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kashe ƴan Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci ƙarya ne – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaɗawa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...
X whatsapp