fidelitybank

Mutum daya ya mutu 8 sun tsira da ransu a hatsarin kwale-kwale

Date:

Wani manomi, a ranar Lahadin da ta gabata, a garin Kabala Doki, dake karamar hukumar Kaduna ta Arewa a jihar Kaduna, ya nutse a cikin ruwa sakamakon hadarin kwale-kwale.

Lamarin ya faru ne da misalin karfe 8:30 na safiyar ranar Lahadin da ta gabata, kamar yadda wata majiya ta bayyana, yayin da wanda aka kashen mai suna Umar, ya taka kwale-kwalen domin taimaka wa mutanen da suka makale a gefen kogin amma kwale-kwalen ya kife.

Ya bayyana cewa wanda aka kashe din ya shahara a cikin al’umma kuma ya mallaki gona kusa da kogin.

Ya ce, “Abin damuwa ne domin Umar ya san yin iyo kuma ya yi noma a bakin kogi tsawon shekaru.

“Wannan ne ya sa muka yi mamakin samun labarin cewa ya nutse a cikin kogi daya a lokacin da yake kokarin ceto mutanen da suka makale a wancan gefen kogin. Allah ya gafarta masa kurakuransa”.

Majiyar ta bayyana cewa dukkan sauran da ke cikin jirgin sun tsira da ransu.

Shugaban karamar hukumar Kaduna ta Arewa, Muktar Baloni, yayin da yake tabbatar da faruwar lamarin, ya bayyana cewa har yanzu ba a gano gawar mamacin ba.

nigeria daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp