Wani manomi, a ranar Lahadin da ta gabata, a garin Kabala Doki, dake karamar hukumar Kaduna ta Arewa a jihar Kaduna, ya nutse a cikin ruwa sakamakon hadarin kwale-kwale.
Lamarin ya faru ne da misalin karfe 8:30 na safiyar ranar Lahadin da ta gabata, kamar yadda wata majiya ta bayyana, yayin da wanda aka kashen mai suna Umar, ya taka kwale-kwalen domin taimaka wa mutanen da suka makale a gefen kogin amma kwale-kwalen ya kife.
Ya bayyana cewa wanda aka kashe din ya shahara a cikin al’umma kuma ya mallaki gona kusa da kogin.
Ya ce, “Abin damuwa ne domin Umar ya san yin iyo kuma ya yi noma a bakin kogi tsawon shekaru.
“Wannan ne ya sa muka yi mamakin samun labarin cewa ya nutse a cikin kogi daya a lokacin da yake kokarin ceto mutanen da suka makale a wancan gefen kogin. Allah ya gafarta masa kurakuransa”.
Majiyar ta bayyana cewa dukkan sauran da ke cikin jirgin sun tsira da ransu.
Shugaban karamar hukumar Kaduna ta Arewa, Muktar Baloni, yayin da yake tabbatar da faruwar lamarin, ya bayyana cewa har yanzu ba a gano gawar mamacin ba.