fidelitybank

Mutum biyar sun mutu a ruwa garin tserewa ‘yan bindiga

Date:

Wasu mutum biyar sun rasa rayukansu yayin da suke kokarin tsere wa masu garkuwa da mutane a kauyen Chakumi na karamar hukumar Abaji a babban birnin tarayyar Najeriya, Abuja.

Cikin wadanda suka rasa rayukan nasu akwai maza biyu da mata uku, a wannan kauye da ke daura da kauyen Daku na karamar hukumar Gwagwalada.

Tabarbarewar matsalar tsaro ta kai ga wasu mazauna kauyukan da ke kananan hukumomin Abaji da Gwagwalada na yin kaura, suna barin gonakinsu babu masu kula da su.

Kamar dai yadda suka saba a wannan lokaci na damina, mutanen kauyen Chakumi da ke karamar hukumar Abaji ta babban birnin Najeriya Abuja, sun fita zuwa gonakinsu da sanyin safiyar ranar Laraba.

Sai dai bayan sun isa gonakin, sun hango masu garkuwa da mutane dauke da muggan makamai, lamarin da ya tilasta musu komawa gida.

Amma duk da sun koma gida – ba su tsira ba, domin masu garkuwa da mutanen sun bisu har kauyen nasu.

Cikin wadanda wannan al’amari ya rutsa da su akwai wata matar aure, baya ga wasu mutum biyu.

Abubakar Abdullahi, wanda tsohon mataimakin shugaban karamar hukumar Abaji ne, ya shaida wa BBC cewa ‘yan uwansa biyu sun halaka a sanadiyyar kokarin tserewa masu garkuwa da mutanen.

Kuma Mallam Abdullahi ya shaida min cewa duk da kusancinsu da babban birnin tarayyar Najeriya, babu wani dauki da suka samu daga hukumimin birnin ko kuma jami’an tsaro.

Ya kuma ce har zuwa yau da rana ba a ga gawar wadanda ruwan kogin Gurara ya ci ba.

DSP Josephine Adeh, kakakin rundunar ‘yan sanda na babban birnin tarayya Abuja ta ce ba ta da cikakken bayani game da wanann harin da masu garkuwa suka kai, amma ta ce za ta bincika kuma za ta sanar da BBC abin da ta gano daga baya.

Matsalar tsaro a wannan yankin da ke kusa da kan iyakar Abuja da JIhar Kogi da kuma karamar hukumar Gwagawalada na kara tabarbarewa, har ya kai ga mazauna kauyukan na yin kaura zuwa wasu yankunan, inda manoma suka bar gonakinsu babu mai kulawa da su.

punch newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp