fidelitybank

Mutum biyar sun mutu a ruwa garin tserewa ‘yan bindiga

Date:

Wasu mutum biyar sun rasa rayukansu yayin da suke kokarin tsere wa masu garkuwa da mutane a kauyen Chakumi na karamar hukumar Abaji a babban birnin tarayyar Najeriya, Abuja.

Cikin wadanda suka rasa rayukan nasu akwai maza biyu da mata uku, a wannan kauye da ke daura da kauyen Daku na karamar hukumar Gwagwalada.

Tabarbarewar matsalar tsaro ta kai ga wasu mazauna kauyukan da ke kananan hukumomin Abaji da Gwagwalada na yin kaura, suna barin gonakinsu babu masu kula da su.

Kamar dai yadda suka saba a wannan lokaci na damina, mutanen kauyen Chakumi da ke karamar hukumar Abaji ta babban birnin Najeriya Abuja, sun fita zuwa gonakinsu da sanyin safiyar ranar Laraba.

Sai dai bayan sun isa gonakin, sun hango masu garkuwa da mutane dauke da muggan makamai, lamarin da ya tilasta musu komawa gida.

Amma duk da sun koma gida – ba su tsira ba, domin masu garkuwa da mutanen sun bisu har kauyen nasu.

Cikin wadanda wannan al’amari ya rutsa da su akwai wata matar aure, baya ga wasu mutum biyu.

Abubakar Abdullahi, wanda tsohon mataimakin shugaban karamar hukumar Abaji ne, ya shaida wa BBC cewa ‘yan uwansa biyu sun halaka a sanadiyyar kokarin tserewa masu garkuwa da mutanen.

Kuma Mallam Abdullahi ya shaida min cewa duk da kusancinsu da babban birnin tarayyar Najeriya, babu wani dauki da suka samu daga hukumimin birnin ko kuma jami’an tsaro.

Ya kuma ce har zuwa yau da rana ba a ga gawar wadanda ruwan kogin Gurara ya ci ba.

DSP Josephine Adeh, kakakin rundunar ‘yan sanda na babban birnin tarayya Abuja ta ce ba ta da cikakken bayani game da wanann harin da masu garkuwa suka kai, amma ta ce za ta bincika kuma za ta sanar da BBC abin da ta gano daga baya.

Matsalar tsaro a wannan yankin da ke kusa da kan iyakar Abuja da JIhar Kogi da kuma karamar hukumar Gwagawalada na kara tabarbarewa, har ya kai ga mazauna kauyukan na yin kaura zuwa wasu yankunan, inda manoma suka bar gonakinsu babu mai kulawa da su.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan Æ´ansanda mai kula da sashen kai É—auki na...

INEC za ta bai wa É—aurarru damar kaÉ—a Æ™uri’a a lokacin zaÉ“uka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

ÆŠaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon É—an takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaÉ—i mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaÉ—i...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp