Hukumar kula da kiyaye hadura ta kasa. FRSC, ta ce hatsarin ya afku ne a lokacin da daya daga cikin motocin ya rasa yadda zai shawo kan motar bayan tsallake wani rami, sannan ya yi karo da daya motar.
Kakakin hukumar a Jigawa, Ibrahim Gambo, ya shaidawa PREMIUM TIMES cewa, tawagar ceto na hukumar ta kwato wadanda lamarin ya rutsa da su daga wurin kuma aka kai su asibiti.
An tabbatar da mutuwar mutane tara tare da jikkata wasu 10 a wani mummunan hatsarin mota da ya afku a ranar Litinin da ta gabata a karamar hukumar Gaya ta jihar Kano.
Hatsarin ya afku ne a wani yanki na babbar hanyar Kano zuwa Maiduguri da ake gyarawa kusa da kauyen Sabaru-Laraba da ke kan iyaka tsakanin jihohin Jigawa da Kano.
Jami’in ya ce, hatsarin ya rutsa da wata motar bas Toyota Hummer, mai lamba DRZ, 846, XA da kuma wata motar bas Toyota Sharon mai rijista Dal, 830, XA.
Jami’in ya ce, akwai maza 17 da mata biyu a cikin motocin biyu. Dukkan wadanda suka mutu maza ne, yayin da mata biyu na cikin wadanda suka samu munanan raunuka.
Da yake tsokaci kan hatsarin, mai taimaka wa shugaban kasa Muhammadu Buhari kan harkokin yada labarai, Bashir Ahmad, a wani sako da ya wallafa a Facebook, ya bayyana hatsarin a matsayin hadari mai muni.
Ahmad, wanda ya fito daga garin Gaya, ya ce, wadanda abin ya shafa ’yan unguwarsu ne, Gaya, wadanda suka je yawon bude ido.
Ya jajantawa Sarkin Gaya, Aliyu Ibrahim, shugaban karamar hukumar Ahmad Tashi, da iyalan wadanda lamarin ya shafa.