fidelitybank

Mutum 9 sun mutu 10 sun jikkata a wani hadari a Kano – FRSC

Date:

Hukumar kula da kiyaye hadura ta kasa. FRSC, ta ce hatsarin ya afku ne a lokacin da daya daga cikin motocin ya rasa yadda zai shawo kan motar bayan tsallake wani rami, sannan ya yi karo da daya motar.

Kakakin hukumar a Jigawa, Ibrahim Gambo, ya shaidawa PREMIUM TIMES cewa, tawagar ceto na hukumar ta kwato wadanda lamarin ya rutsa da su daga wurin kuma aka kai su asibiti.

An tabbatar da mutuwar mutane tara tare da jikkata wasu 10 a wani mummunan hatsarin mota da ya afku a ranar Litinin da ta gabata a karamar hukumar Gaya ta jihar Kano.

Hatsarin ya afku ne a wani yanki na babbar hanyar Kano zuwa Maiduguri da ake gyarawa kusa da kauyen Sabaru-Laraba da ke kan iyaka tsakanin jihohin Jigawa da Kano.

Jami’in ya ce, hatsarin ya rutsa da wata motar bas Toyota Hummer, mai lamba DRZ, 846, XA da kuma wata motar bas Toyota Sharon mai rijista Dal, 830, XA.

Jami’in ya ce, akwai maza 17 da mata biyu a cikin motocin biyu. Dukkan wadanda suka mutu maza ne, yayin da mata biyu na cikin wadanda suka samu munanan raunuka.

Da yake tsokaci kan hatsarin, mai taimaka wa shugaban kasa Muhammadu Buhari kan harkokin yada labarai, Bashir Ahmad, a wani sako da ya wallafa a Facebook, ya bayyana hatsarin a matsayin hadari mai muni.

Ahmad, wanda ya fito daga garin Gaya, ya ce, wadanda abin ya shafa ’yan unguwarsu ne, Gaya, wadanda suka je yawon bude ido.

Ya jajantawa Sarkin Gaya, Aliyu Ibrahim, shugaban karamar hukumar Ahmad Tashi, da iyalan wadanda lamarin ya shafa.

latest news in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na É—aukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

ÆŠanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa Æ´an Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa Æ´anbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen Æ™auyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faÉ—a ADC

Tsohon É—an jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

ÆŠan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp