fidelitybank

Mutum 9 sun mutu 10 sun jikkata a wani hadari a Kano – FRSC

Date:

Hukumar kula da kiyaye hadura ta kasa. FRSC, ta ce hatsarin ya afku ne a lokacin da daya daga cikin motocin ya rasa yadda zai shawo kan motar bayan tsallake wani rami, sannan ya yi karo da daya motar.

Kakakin hukumar a Jigawa, Ibrahim Gambo, ya shaidawa PREMIUM TIMES cewa, tawagar ceto na hukumar ta kwato wadanda lamarin ya rutsa da su daga wurin kuma aka kai su asibiti.

An tabbatar da mutuwar mutane tara tare da jikkata wasu 10 a wani mummunan hatsarin mota da ya afku a ranar Litinin da ta gabata a karamar hukumar Gaya ta jihar Kano.

Hatsarin ya afku ne a wani yanki na babbar hanyar Kano zuwa Maiduguri da ake gyarawa kusa da kauyen Sabaru-Laraba da ke kan iyaka tsakanin jihohin Jigawa da Kano.

Jami’in ya ce, hatsarin ya rutsa da wata motar bas Toyota Hummer, mai lamba DRZ, 846, XA da kuma wata motar bas Toyota Sharon mai rijista Dal, 830, XA.

Jami’in ya ce, akwai maza 17 da mata biyu a cikin motocin biyu. Dukkan wadanda suka mutu maza ne, yayin da mata biyu na cikin wadanda suka samu munanan raunuka.

Da yake tsokaci kan hatsarin, mai taimaka wa shugaban kasa Muhammadu Buhari kan harkokin yada labarai, Bashir Ahmad, a wani sako da ya wallafa a Facebook, ya bayyana hatsarin a matsayin hadari mai muni.

Ahmad, wanda ya fito daga garin Gaya, ya ce, wadanda abin ya shafa ’yan unguwarsu ne, Gaya, wadanda suka je yawon bude ido.

Ya jajantawa Sarkin Gaya, Aliyu Ibrahim, shugaban karamar hukumar Ahmad Tashi, da iyalan wadanda lamarin ya shafa.

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuÉ—in...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaÉ—an wajen tsaron Æ™asa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haÉ—in...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar Æ´an Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaÉ“e shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp