Gwamna jihar Kaduna, Nasir Ahmad El-Rufai, ya karbi kunshin bayanan rahoto kan harkokin tsaro na shekarar 2021.
Kwamashinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida, Samuel Aruwan ne ya gabatar da rahoton a fadar gwamnatin jihar, a wani taro da ya samu wakilcin kwamandojin rundunar sojan Najeriya da ke jihar.
Rahoton 2020 ya nuna cewa rikici ya kashe mutum 937 a Kaduna yayin da aka yi garkuwa da 1,972. Cikin rahoton har da na wata ukun karshen 2021.