fidelitybank

Mutane 91 sun mutu a ambaliyar ruwan Bayelsa

Date:

Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Bayelsa (BYSEMA), ta bayyana cewa akalla mutane casa’in da shida ne suka rasa rayukansu, inda jimillar mutane miliyan daya da dubu dari uku da arba’in da hudu da goma sha hudu suka shafa kai tsaye sakamakon mummunar ambaliyar ruwa a jihar.

Wani bayanan hukuma da aka fitar a ranar litinin ya kuma nuna cewa, mutane miliyan daya da dubu dari biyu da goma da dari da tamanin da uku ne suka rasa matsugunansu.

DAILY POST ta tattaro cewa Yenagoa, babban birnin jihar, ya yi sanadiyar mutuwar mutane 26 wanda shine adadi mafi yawa da aka samu ya zuwa yanzu.

Da yake tabbatar da bayanan, Shugaban Hukumar SEMA na Jiha, Hon. Walaman Igrubia, ya ce har yanzu ana ci gaba da tattara bayanai daga filin, yayin da yake lura da cewa ambaliyar ruwan ta shafi filayen noma da dama, gine-ginen makarantu, gine-ginen kiwon lafiya da dai sauransu.

Ya kuma tabbatar da cewa ambaliyar ta shafi al’ummomi da dama a daukacin kananan hukumomin jihar 8.

Igrubia ya bayyana karara cewa rahotannin farko da bayanan da hukumar SEMA da sauran hukumomi ke bayarwa sun nuna cewa jihar Bayelsa ce ta fi fama da ambaliyar ruwa a tsakanin Jihohin kasar nan.

Shugaban Hukumar ta SEMA ya bayyana cewa ya ji dadin jin cewa Ministar Harkokin Agaji, Gudanar da Masifu da Cigaban Jama’a, Hajiya Sadiya Farouq, yanzu ta amince da cewa Jihar Bayelsa tana cikin jerin Jihohi goma da suka fi fama da matsalar.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp