fidelitybank

Mutane 8 sun mutu yayin da wasu suka jikkata a hadarin Bauchi – FRSC

Date:

Kwamandan hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) a jihar Bauchi, Yusuf Abdullahi, ya ce mutane takwas ne suka rasa rayukansu a wani hadarin mota karo na biyu da aka samu ranar Alhamis a jihar.

Kwamandan sashin, Yusuf Abdullahi, ya tabbatarwa da kamfanin dillancin labarai na kasa NAN, faruwar lamarin a ranar Juma’a a Bauchi.

Hatsarin ya afku ne sa’o’i 11 bayan da mutane bakwai suka rasa rayukansu, sannan wasu biyu suka jikkata a wani mummunan hatsarin mota da ya afku a hanyar Bauchi zuwa Jos.

Abdullahi ya ce, “Wasu hudu sun samu raunuka daban-daban a hadarin wanda ya afku a kauyen Kafin Liman Daura da hanyar Bauchi zuwa Kano da misalin karfe 11:30 na dare.

Ya kuma ce, “Hatsarin ya hada da wata mota kirar lamba KMC95YU, motar bas kirar Galaxy Ford mai lamba NNG21MG da wata mota kirar Opel Vectra mai lamba BAU490AA”.

Kwamandan ya ce, “Mutane 12 ne hatsarin ya rutsa da su wanda suka hada da manya maza da mata uku. Takwas sun mutu nan take, sun hada da maza biyar da mata uku. Maza hudu sun samu munanan raunuka.

“Motar ta lalace kuma ba ta tsaya yadda ya kamata ba wanda hakan ya kawo cikas a kan hanyar kuma sauran motocin sun shiga cikinta, saboda rashin kulawa,” in ji shi.

Ya ce tuni an garzaya da wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin Kafin Madaki, domin yi musu magani yayin da aka ajiye gawarwakin a dakin ajiye gawa da ke cikin dakin.

Kwamandan ya shawarci masu ababen hawa da su kiyaye ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa a jihar.

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...
X whatsapp