fidelitybank

Mutane 8 sun mutu yayin da wasu suka jikkata a hadarin Bauchi – FRSC

Date:

Kwamandan hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) a jihar Bauchi, Yusuf Abdullahi, ya ce mutane takwas ne suka rasa rayukansu a wani hadarin mota karo na biyu da aka samu ranar Alhamis a jihar.

Kwamandan sashin, Yusuf Abdullahi, ya tabbatarwa da kamfanin dillancin labarai na kasa NAN, faruwar lamarin a ranar Juma’a a Bauchi.

Hatsarin ya afku ne sa’o’i 11 bayan da mutane bakwai suka rasa rayukansu, sannan wasu biyu suka jikkata a wani mummunan hatsarin mota da ya afku a hanyar Bauchi zuwa Jos.

Abdullahi ya ce, “Wasu hudu sun samu raunuka daban-daban a hadarin wanda ya afku a kauyen Kafin Liman Daura da hanyar Bauchi zuwa Kano da misalin karfe 11:30 na dare.

Ya kuma ce, “Hatsarin ya hada da wata mota kirar lamba KMC95YU, motar bas kirar Galaxy Ford mai lamba NNG21MG da wata mota kirar Opel Vectra mai lamba BAU490AA”.

Kwamandan ya ce, “Mutane 12 ne hatsarin ya rutsa da su wanda suka hada da manya maza da mata uku. Takwas sun mutu nan take, sun hada da maza biyar da mata uku. Maza hudu sun samu munanan raunuka.

“Motar ta lalace kuma ba ta tsaya yadda ya kamata ba wanda hakan ya kawo cikas a kan hanyar kuma sauran motocin sun shiga cikinta, saboda rashin kulawa,” in ji shi.

Ya ce tuni an garzaya da wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin Kafin Madaki, domin yi musu magani yayin da aka ajiye gawarwakin a dakin ajiye gawa da ke cikin dakin.

Kwamandan ya shawarci masu ababen hawa da su kiyaye ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa a jihar.

breaking news in nigeria today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...
X whatsapp