Kwamandan hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) a jihar Bauchi, Yusuf Abdullahi, ya ce mutane takwas ne suka rasa rayukansu a wani hadarin mota karo na biyu da aka samu ranar Alhamis a jihar.
Kwamandan sashin, Yusuf Abdullahi, ya tabbatarwa da kamfanin dillancin labarai na kasa NAN, faruwar lamarin a ranar Juma’a a Bauchi.
Hatsarin ya afku ne sa’o’i 11 bayan da mutane bakwai suka rasa rayukansu, sannan wasu biyu suka jikkata a wani mummunan hatsarin mota da ya afku a hanyar Bauchi zuwa Jos.
Abdullahi ya ce, “Wasu hudu sun samu raunuka daban-daban a hadarin wanda ya afku a kauyen Kafin Liman Daura da hanyar Bauchi zuwa Kano da misalin karfe 11:30 na dare.
Ya kuma ce, “Hatsarin ya hada da wata mota kirar lamba KMC95YU, motar bas kirar Galaxy Ford mai lamba NNG21MG da wata mota kirar Opel Vectra mai lamba BAU490AA”.
Kwamandan ya ce, “Mutane 12 ne hatsarin ya rutsa da su wanda suka hada da manya maza da mata uku. Takwas sun mutu nan take, sun hada da maza biyar da mata uku. Maza hudu sun samu munanan raunuka.
“Motar ta lalace kuma ba ta tsaya yadda ya kamata ba wanda hakan ya kawo cikas a kan hanyar kuma sauran motocin sun shiga cikinta, saboda rashin kulawa,” in ji shi.
Ya ce tuni an garzaya da wadanda suka jikkata zuwa babban asibitin Kafin Madaki, domin yi musu magani yayin da aka ajiye gawarwakin a dakin ajiye gawa da ke cikin dakin.
Kwamandan ya shawarci masu ababen hawa da su kiyaye ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa a jihar.