fidelitybank

Murnar cika shekaru 79: Idan n agama mulki zan koma gona ta – Buhari

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yi bikin cika shekaru 79 a duniya a birnin Santambul ta kasar Turkiyya.

Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, Garba Shehu, ya ce an yi bikin murnar cikar shekarun ne ta musamman.

A cikin wata sanarwa da PlatinumPost ta samu, Garba Shehu, ya ce: “A ranar cikarsa shekaru 79 a duniya, yau Juma’a a birnin Santambull ta kasar Turkiyya, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yanka Buredin “Cake” a kan zagayowar ranar haihuwar sa, mai launin kore-fari-kore, kai tsaye ya nufi kujera ya na shirin ganawa da jami’ai a cikin tawagarsa, sannan kuma ya wuce fadar Dolmabahce, domin ganawa da takwaransa na Turkiyya Recep Tayyip Erdogan”.

A martanin karramawar da a ka yi a madadin ministoci da sauran tawagar da Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama ya yi, shugaba Buhari, ya ce, zai yi iya bakin kokarinsa ga Najeriya har zuwa ranar karshe da za a yi zabe a 2023. Ya mika wa magajinsa ya koma gonarsa ya yi noma da kiwo.

Mai magana da yawun shugaban ya rawaito Buhari ya na cewa “Na yi tunanin cewa na yi nisa daga Abuja zan tsere wa wadannan abubuwa. Domin sun gaya mani abin da su ke son yi a wannan rana, sai ga shi yanzu a nan kuna yin wannan abun.

 

“Ina fatan shekarar 2023 idan na gama, in koma gida in ci gaba da aikin gona ta. Daga yanzu zuwa wancan lokaci, zan yi iya kokari na wajen ciyar da kasa da al’ummarta gaba, da gudanar da ayyuka na kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ya tanada”. Inji Buhari.

daily post nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp