Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yi bikin cika shekaru 79 a duniya a birnin Santambul ta kasar Turkiyya.
Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, Garba Shehu, ya ce an yi bikin murnar cikar shekarun ne ta musamman.
A cikin wata sanarwa da PlatinumPost ta samu, Garba Shehu, ya ce: “A ranar cikarsa shekaru 79 a duniya, yau Juma’a a birnin Santambull ta kasar Turkiyya, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yanka Buredin “Cake” a kan zagayowar ranar haihuwar sa, mai launin kore-fari-kore, kai tsaye ya nufi kujera ya na shirin ganawa da jami’ai a cikin tawagarsa, sannan kuma ya wuce fadar Dolmabahce, domin ganawa da takwaransa na Turkiyya Recep Tayyip Erdogan”.
A martanin karramawar da a ka yi a madadin ministoci da sauran tawagar da Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama ya yi, shugaba Buhari, ya ce, zai yi iya bakin kokarinsa ga Najeriya har zuwa ranar karshe da za a yi zabe a 2023. Ya mika wa magajinsa ya koma gonarsa ya yi noma da kiwo.
Mai magana da yawun shugaban ya rawaito Buhari ya na cewa “Na yi tunanin cewa na yi nisa daga Abuja zan tsere wa wadannan abubuwa. Domin sun gaya mani abin da su ke son yi a wannan rana, sai ga shi yanzu a nan kuna yin wannan abun.
“Ina fatan shekarar 2023 idan na gama, in koma gida in ci gaba da aikin gona ta. Daga yanzu zuwa wancan lokaci, zan yi iya kokari na wajen ciyar da kasa da al’ummarta gaba, da gudanar da ayyuka na kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ya tanada”. Inji Buhari.