fidelitybank

Murnar cika shekaru 79: Idan n agama mulki zan koma gona ta – Buhari

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya yi bikin cika shekaru 79 a duniya a birnin Santambul ta kasar Turkiyya.

Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai da wayar da kan jama’a, Garba Shehu, ya ce an yi bikin murnar cikar shekarun ne ta musamman.

A cikin wata sanarwa da PlatinumPost ta samu, Garba Shehu, ya ce: “A ranar cikarsa shekaru 79 a duniya, yau Juma’a a birnin Santambull ta kasar Turkiyya, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yanka Buredin “Cake” a kan zagayowar ranar haihuwar sa, mai launin kore-fari-kore, kai tsaye ya nufi kujera ya na shirin ganawa da jami’ai a cikin tawagarsa, sannan kuma ya wuce fadar Dolmabahce, domin ganawa da takwaransa na Turkiyya Recep Tayyip Erdogan”.

A martanin karramawar da a ka yi a madadin ministoci da sauran tawagar da Ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama ya yi, shugaba Buhari, ya ce, zai yi iya bakin kokarinsa ga Najeriya har zuwa ranar karshe da za a yi zabe a 2023. Ya mika wa magajinsa ya koma gonarsa ya yi noma da kiwo.

Mai magana da yawun shugaban ya rawaito Buhari ya na cewa “Na yi tunanin cewa na yi nisa daga Abuja zan tsere wa wadannan abubuwa. Domin sun gaya mani abin da su ke son yi a wannan rana, sai ga shi yanzu a nan kuna yin wannan abun.

 

“Ina fatan shekarar 2023 idan na gama, in koma gida in ci gaba da aikin gona ta. Daga yanzu zuwa wancan lokaci, zan yi iya kokari na wajen ciyar da kasa da al’ummarta gaba, da gudanar da ayyuka na kamar yadda kundin tsarin mulkin kasa ya tanada”. Inji Buhari.

the nation news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp