Gwamnatin Jihar Zamfara ta nemi afuwa kan rufe kafofin yaɗa larabai shida da ta yi.
Jaridar The Cable a Najeriya ta ruwaito cewa gwamnatin jihar ta bayar da umurnin rufe wasu kafofin yada labarai a Gusau, babban birnin jihar saboda yada shiri ka yakin neman zabe da Jam’iyyar PDP ta gudanar.
Kafofi yaɗa labaran da abin ya shafa sun ƙunshi Radio Najeriya, da Pride FM Gusau, da NTA Gusau, da Gamji Talabijin, da Vision FM, da Al Umma TV.
Wannan na zuwa ne bayan da gwamna Bello Matawalle ya sanar da dokar kulle a kananan hukumomin Anka da Bukkuyum da kuma Gummi na jihar bayan ɗawowar hare-haren ‘yan bindiga.
Gwamna Matawalle ya kuma bayar da umurnin dakatar da tarukan siyasa a kananan hukumomin da abin ya shafa.
Shima da yake magana kan batun, Abdullahi Shinkafi, shugaban kwamitin hukunta ‘yan bindiga da sauran masu aikata laifi, ya nemi afuwar kafofin yada labaran yayin tattaunawa da manema labarai a jiya Litinin.
Shinkafi ya ce tuni gwamnati ta janye umurnin da kwamishinan ‘yan sanda ya bayar na kamawa tare da hukunta mutane da aka gani a kafofin yaɗa labaran.
Ya kuma bukaci gidajen yaɗa labaran da kuma ‘yan jarida da su mutunta dokokin jihar da kuma taimaka wa gwamnati a kokarinta na dakile ayyukan ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane.