Kimanin kungiyoyi 28 daga sassan Najeriya ne suka hallara a Kano domin bayyana goyon bayansu ga mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbanjo da ya tsaya takarar shugaban kasa a zaben 2023 mai zuwa.
Taron wanda ya hada kungiyoyin a karkashin wata inuwa mai suna ‘The New Tribe’, ya ga tawagogi daga dukkan shiyyoyin siyasar kasar nan, sun taru domin nuna goyon bayansu ga Osinbajo, wanda har yanzu bai nuna sha’awar tsayawa takara ba a hukumance.
Dailytrust ta rawaito cewa, a nasu jawabin, tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano, Farfesa Hafiz Abubakar, da dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tarauni, Hafizu Kawu, sun bayyana cewa, hawan Osinbajo ba wai son rai ba ne, ko kuma son kasa, sai dai sakamakon kwarewarsa na ban mamaki.
Sun bayyana shi a matsayin haziki mai kishi, mai kyakkyawar niyya da hikima da alheri wajen bayyana su ta hanyoyin da suka zaburar da miliyoyin mutane a fadin kasar nan.
Ko’odinetan kungiyoyin, Anwar Hassan, ya ce, sun taru ne domin bayyana wa Osinbajo kashi 100 bisa 100 na cancantar sa wanda tun daga lokacin da ya samu nasarar yi wa kasa hidima a matsayin mataimakin shugaban kasa.
A nasa jawabin, tsohon dan majalisar dattawa mai wakiltar Osun ta tsakiya, Farfesa Sola Adeyeye, ya ce“Najeriya ta dade ta na kira da a kafa wata sabuwar kabila, wanda ba a janye kowa ba, saboda bambancin kabila ko addini sama da shekaru sittin”.
Da ya ke magana kan dalilin da ya sa sabuwar kabilar ta zabi Kano a matsayin wurin kaddamar da ita, Adeyeye ya bayyana jihar Kano a matsayin birni mai cikakkiyar juna biyu, tare da sauran garuruwan da ke cikin cikinta.