fidelitybank

Mun sauya fasalin kudi saboda barayin da suka boye su – Buhari

Date:

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya tabbatar wa da ‘yan ƙasa cewa, gwamnati za ta tabbatar da cewa, ‘yan ƙasa ba su sha wahala ba ta fuskar kasuwancinsu, da kuma samun tsaiko wajen musanya tsofiin takardun kuɗinsu da sabbi a yayin da wa’adin da babban bankin ƙasar ya saka ke ƙara ƙaratowa.

Yayin da yake martani game da rahotonni dogayen layukan mutanen da ke shafe sa’o’i domin samun musanya tsoffin kuɗinsu a bankuna, lamarin da ya janyo suka daga ɓangarorin adawa a ƙasar.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar Mallam Garba Shehu ya fitar, shugaba Buhari ya jaddada cewa an fito da batun sauya fasalin kuɗin ƙasar ne domin yin maganin mutanen da suka ɓoye kuɗin haram, ba don cutar da talaka ba.

Ya kuma ce hakan zai magance matsalar cin hanci da rashawa da ɗaukar nauyin ta’addanci da satar mutane domin karɓar kuɗin fansa.

Shugaba Buhari ya kuma ce tsarin zai taimaka wajen ƙarfafa tattalin arzikin ƙasar

Game da wahalhalun da talakawa ke sha na musanya kuɗaɗensu kuwa, shugaba Buhari ya tabbatar da cewa gwamnati za ta yi iya bakin ƙoƙarinta domin taimaka musu wajen musanya kuɗaɗensu.

Ya kuma jaddada cewa babban bankin ƙasar da sauran bankunan ƙasar sun ƙara haɓaka hanyoyin musanya wa mutane kuɗaɗensu domin tabbatar da cewa an musanya wa kowa kuɗinsa kafin cikar wa’adin.

Babban bankin ƙasar dai ya saka ranar 31 ga watan Janairu a matsayin ranar ƙarshe ta daina amfani da tsoffin takardun kuɗi na 200 da 500 da kuma 1000 a faɗin ƙasar.

mmm.nnn.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...
X whatsapp