fidelitybank

Mun kama masu laifi 245 a kwanaki 40 a Kano — Ƴan Sanda

Date:

 

Rundunar Ƴan Sanda ta Jihar Kano ta ce ta kama ɓatagari da a ke zargin su da aikata manyan laifuka su 245 a kwanaki 40 da su ka gabata.

Kwamishinan Ƴan Sanda na jihar, Sama’ila Shu’aibu Dikko ne ya baiyana hakan a taron manema labarai a shalkwatar rundunar a ranar Alhamis.

Ya ce kamen wani ɓangare ne na ƙoƙarin da rundunar ta ke yi na yaƙi da aikata laifuka a faɗin jihar.

“A ƙoƙarin mu na samar da zaman lafiya ga al’umma, mun dage wajen samar da zaman lafiya a cikin al’umma tare da haɗin kan su. Mu na amfani da bayanan sirri da kuma sintiri, mu yi gaggawar kai ɗauki in da a ka kira mu idan matsala ta afku, mun aiki daidai da yadda ƙa’idojin aikin ƴan sanda ya ke a doka, mu na haɗa kai da sauran hukumomin tsaro, sannan kuma mun yi riƙo da Sintirin nan na Kan ka ce kwabo wanda mu ke ganin alfanon sa sosai,” in ji Kwamishinan.

Da ga masu laifukan da rundunar ta kama a kwai ƴan fashi, masu garkuwa da mutane, ɓarayin shanu, ɓarayin mota, ƴan daba da kuma ƴan shaye-shayen miyagun ƙwayoyi.

Haka-zalika rundunar ta sanar da kuɓutar da mutane 6 da ga hannun masu garkuwa da mutane.

nnn-news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

Ɗan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...
X whatsapp