fidelitybank

Mun kama masu laifi 245 a kwanaki 40 a Kano — Ƴan Sanda

Date:

 

Rundunar Ƴan Sanda ta Jihar Kano ta ce ta kama ɓatagari da a ke zargin su da aikata manyan laifuka su 245 a kwanaki 40 da su ka gabata.

Kwamishinan Ƴan Sanda na jihar, Sama’ila Shu’aibu Dikko ne ya baiyana hakan a taron manema labarai a shalkwatar rundunar a ranar Alhamis.

Ya ce kamen wani ɓangare ne na ƙoƙarin da rundunar ta ke yi na yaƙi da aikata laifuka a faɗin jihar.

“A ƙoƙarin mu na samar da zaman lafiya ga al’umma, mun dage wajen samar da zaman lafiya a cikin al’umma tare da haɗin kan su. Mu na amfani da bayanan sirri da kuma sintiri, mu yi gaggawar kai ɗauki in da a ka kira mu idan matsala ta afku, mun aiki daidai da yadda ƙa’idojin aikin ƴan sanda ya ke a doka, mu na haɗa kai da sauran hukumomin tsaro, sannan kuma mun yi riƙo da Sintirin nan na Kan ka ce kwabo wanda mu ke ganin alfanon sa sosai,” in ji Kwamishinan.

Da ga masu laifukan da rundunar ta kama a kwai ƴan fashi, masu garkuwa da mutane, ɓarayin shanu, ɓarayin mota, ƴan daba da kuma ƴan shaye-shayen miyagun ƙwayoyi.

Haka-zalika rundunar ta sanar da kuɓutar da mutane 6 da ga hannun masu garkuwa da mutane.

vgn news today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp