fidelitybank

Mu kungiyoyi ne na duniya da dangogin mu dake tallafa mana – IPOB

Date:

Haramtacciyar kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB) a ranar Talata ta ce magoya bayanta na gida da na waje sun kasance tushen daukar nauyin su.

Sakatariyar yada labaran kungiyar, Emma Powerful ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

Ya ce, “A karo na goma sha uku, babu wani mutum daya da zai iya daukar nauyin kungiyar IPOB. Mu ƙungiyoyi ne na duniya kuma miliyoyin dangin mu a gida da waje sun kasance tushen tallafin mu.

“Ba mu taba boye wannan gaskiyar ba, saboda mu ba kungiya ce ta sirri ko ta’addanci ba. IPOB ta na da tushe mai kyau kuma ba ma bukatar wani Okorocha ko Uche Nwosu ko Hope Uzodinma ko wani dan siyasa kan lamarin ya dauki nauyin mu. Ba mu da mu’amala da gurbatattun ‘yan siyasa da mutanen da ke da shakku kan tushen arzikin su.” inji IPOB.

In za a iya tunawa cewa, IPOB kungiya ce mai fafutukar neman ballewa a Najeriya, babban burinta shi ne dawo da kasar Biafra mai cin gashin kanta a tsohon yankin Gabashin Najeriya, wanda ya kunshi yankunan Kudu maso Gabas da Kudu-maso-Kudu a yau; ta hanyar zaben raba gardama na ‘yancin kai.

An kafa kungiyar ne a shekarar 2012 a hannun Nnamdi Kanu, dan gwagwarmayar siyasar Najeriya dan kasar Birtaniya wanda ya yi fice wajen fafutukar neman ‘yancin kasar Biafra.

breaking news in nigeria today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...

An gargadi Borno da Yobe da Jigawa su zama cikin shirin ambaliya

Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da...
X whatsapp