fidelitybank

Mu kungiyoyi ne na duniya da dangogin mu dake tallafa mana – IPOB

Date:

Haramtacciyar kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB) a ranar Talata ta ce magoya bayanta na gida da na waje sun kasance tushen daukar nauyin su.

Sakatariyar yada labaran kungiyar, Emma Powerful ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

Ya ce, “A karo na goma sha uku, babu wani mutum daya da zai iya daukar nauyin kungiyar IPOB. Mu ƙungiyoyi ne na duniya kuma miliyoyin dangin mu a gida da waje sun kasance tushen tallafin mu.

“Ba mu taba boye wannan gaskiyar ba, saboda mu ba kungiya ce ta sirri ko ta’addanci ba. IPOB ta na da tushe mai kyau kuma ba ma bukatar wani Okorocha ko Uche Nwosu ko Hope Uzodinma ko wani dan siyasa kan lamarin ya dauki nauyin mu. Ba mu da mu’amala da gurbatattun ‘yan siyasa da mutanen da ke da shakku kan tushen arzikin su.” inji IPOB.

In za a iya tunawa cewa, IPOB kungiya ce mai fafutukar neman ballewa a Najeriya, babban burinta shi ne dawo da kasar Biafra mai cin gashin kanta a tsohon yankin Gabashin Najeriya, wanda ya kunshi yankunan Kudu maso Gabas da Kudu-maso-Kudu a yau; ta hanyar zaben raba gardama na ‘yancin kai.

An kafa kungiyar ne a shekarar 2012 a hannun Nnamdi Kanu, dan gwagwarmayar siyasar Najeriya dan kasar Birtaniya wanda ya yi fice wajen fafutukar neman ‘yancin kasar Biafra.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp