fidelitybank

Mazauna Ketare: ‘Yan Najeriya miliyan 1.5 a Italiya ba su da fasfo – NIDOE

Date:

Kungiyar ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje, a nahiyar Turai (NIDOE), reshen kasar Italiya, ta ce kimanin mutane miliyan 1.5 daga cikin miliyan 3 da su ka yi wa rijista a Italiya na fama da karancin fasfo din Najeriya.

Shugaban kungiyar, George Omo-Iduhon, ya bayyana haka a zantawarsa da manema labarai yayin da ya ke tunani kan ayyukan NIDOE a Turai da Italiya.

An amince da NIDOE a matsayin dandalin hukuma wanda ’yan Najeriya mazauna kasashen waje za su iya gabatar da kokarinsu na ci gaba a Najeriya.

Ƙungiyar ta na haɗin gwiwa tare da al’ummar Najeriya da ƙungiyoyin ƙwararru da kuma kasuwancin jama’a da masu zaman kansu a cikin wuraren da a ka mayar da hankali kamar su ƙwararrun a saka hannun jari na waje (FDI) da shawarwarin masu ruwa da tsaki da ayyukan likitanci da tallafin ilimi da kwarewa wajen sauya wurare zuwa Najeriya.

A cewar, Omo-Iduhon, akwai ‘yan Najeriya da ya wa a Italiya fiye da sauran kasashen Turai, kuma ‘yan Najeriya da su ka yi rijista bisa ga alkaluma sun kai miliyan 3 baya ga wadanda ba su da takardun shaidar izini.

“Daya daga cikin manyan matsalolin da ‘yan Najeriya mazauna Italiya ke fuskanta shi ne, karancin fasfo din Najeriya da zai taimaka wajen saukaka zirga-zirga da izinin aiki.

“Ya kamata gwamnatin Najeriya ta taimaka wajen magance wannan matsala mai cike da rudani, domin kasar Italiya ita ce hanyar shiga wasu kasashen Turai musamman ‘yan Najeriya.

“Kusan ‘yan Najeriya miliyan 1.5 a Italiya ba su da fasfo, har ma da wasu daga cikin wadanda gwamnatin Italiya ta karba ba a ba su fasfo na Najeriya ba, wanda ke da wahala su yi aiki a kasar”. Inji Omo-Iduhuon.

Ya ce kungiyar ta himmatu wajen bunkasa tattalin arzikin Najeriya, ya kara da cewa dole ne mambobin kungiyar su yi iya kokarinsu na komawa gida domin gina Najeriya.

 

A cewarsa, yawancin ‘yan Najeriya a Italiya suna da halaltaccen kasuwanci kuma ‘yan Italiya sun kasance masu karbar baki.

 

vanguard new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp