fidelitybank

Mazauna Ketare: ‘Yan Najeriya miliyan 1.5 a Italiya ba su da fasfo – NIDOE

Date:

Kungiyar ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje, a nahiyar Turai (NIDOE), reshen kasar Italiya, ta ce kimanin mutane miliyan 1.5 daga cikin miliyan 3 da su ka yi wa rijista a Italiya na fama da karancin fasfo din Najeriya.

Shugaban kungiyar, George Omo-Iduhon, ya bayyana haka a zantawarsa da manema labarai yayin da ya ke tunani kan ayyukan NIDOE a Turai da Italiya.

An amince da NIDOE a matsayin dandalin hukuma wanda ’yan Najeriya mazauna kasashen waje za su iya gabatar da kokarinsu na ci gaba a Najeriya.

Ƙungiyar ta na haɗin gwiwa tare da al’ummar Najeriya da ƙungiyoyin ƙwararru da kuma kasuwancin jama’a da masu zaman kansu a cikin wuraren da a ka mayar da hankali kamar su ƙwararrun a saka hannun jari na waje (FDI) da shawarwarin masu ruwa da tsaki da ayyukan likitanci da tallafin ilimi da kwarewa wajen sauya wurare zuwa Najeriya.

A cewar, Omo-Iduhon, akwai ‘yan Najeriya da ya wa a Italiya fiye da sauran kasashen Turai, kuma ‘yan Najeriya da su ka yi rijista bisa ga alkaluma sun kai miliyan 3 baya ga wadanda ba su da takardun shaidar izini.

“Daya daga cikin manyan matsalolin da ‘yan Najeriya mazauna Italiya ke fuskanta shi ne, karancin fasfo din Najeriya da zai taimaka wajen saukaka zirga-zirga da izinin aiki.

“Ya kamata gwamnatin Najeriya ta taimaka wajen magance wannan matsala mai cike da rudani, domin kasar Italiya ita ce hanyar shiga wasu kasashen Turai musamman ‘yan Najeriya.

“Kusan ‘yan Najeriya miliyan 1.5 a Italiya ba su da fasfo, har ma da wasu daga cikin wadanda gwamnatin Italiya ta karba ba a ba su fasfo na Najeriya ba, wanda ke da wahala su yi aiki a kasar”. Inji Omo-Iduhuon.

Ya ce kungiyar ta himmatu wajen bunkasa tattalin arzikin Najeriya, ya kara da cewa dole ne mambobin kungiyar su yi iya kokarinsu na komawa gida domin gina Najeriya.

 

A cewarsa, yawancin ‘yan Najeriya a Italiya suna da halaltaccen kasuwanci kuma ‘yan Italiya sun kasance masu karbar baki.

 

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp