fidelitybank

Mayaƙan Boko Haram sun ajiye makamai a Gwoza, yayin da dakarun Nijeriya su ka fafata da ISWAP a Malam Fatori

Date:

An samu ƙarin wasu mayaƙan Boko Haram sun miƙa kansu ga dakarun Nijeriya a jiya Laraba da safe, inda da yamma kuma dakarun Nijeriya su ka fafata da mayaƙan ISWAP a Malam Fatori.

Kwamndojin Boko Haram da ƴan barandansu ne dai su ka miƙa kansu da ajiye makamai ga dakarun gwamnatin Nijeriya, duk da ISWAP ta yi yunƙurin ta hana faruwar hakan.
Majiyar sirri ta sojojin Nijeriya ta baiyanawa PRNigeria cewa za a samu ƙarin ƴan Boko Haram da za su miƙa kansu zuwa ƙarshen shekara.

“Wasu daga cikin kwamndojin mayaƙan Boko Haram da ƴan barandansu sun tsere daga yankin Jaje a dajin Sambisa, in da tuni su ka miƙa kansu ga dakarun rundunar soji ta 192 da ke Gwoza-Limankara a Jihar Borno.

“Yawancinsu tirsasa su a ka yi su ka shiga Boko Haram lokacin su na ƙanana.
“A yanzu haka sama da mayaƙan Boko Haram 17,000 ne su ka saduda duk da yunƙuri da ISWAP ke yi ta daƙile su daga miƙa kansu,” in ji jami’in tsaron.

Haka-zalika PRNigeria ta jiyo cewa dakarun Nijeriya na nan na fafatawa da mayaƙan ISWAP a daren Laraba a Malam Fatori.

Malam Fatori ya zama yankin da ISWAP ta fi ƙarfi inda har ta kafa ma majalisar shura a yankin wanda ya ke bida da Ƙasar Nijer.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp