fidelitybank

Mayaƙan Boko Haram sun ajiye makamai a Gwoza, yayin da dakarun Nijeriya su ka fafata da ISWAP a Malam Fatori

Date:

An samu ƙarin wasu mayaƙan Boko Haram sun miƙa kansu ga dakarun Nijeriya a jiya Laraba da safe, inda da yamma kuma dakarun Nijeriya su ka fafata da mayaƙan ISWAP a Malam Fatori.

Kwamndojin Boko Haram da ƴan barandansu ne dai su ka miƙa kansu da ajiye makamai ga dakarun gwamnatin Nijeriya, duk da ISWAP ta yi yunƙurin ta hana faruwar hakan.
Majiyar sirri ta sojojin Nijeriya ta baiyanawa PRNigeria cewa za a samu ƙarin ƴan Boko Haram da za su miƙa kansu zuwa ƙarshen shekara.

“Wasu daga cikin kwamndojin mayaƙan Boko Haram da ƴan barandansu sun tsere daga yankin Jaje a dajin Sambisa, in da tuni su ka miƙa kansu ga dakarun rundunar soji ta 192 da ke Gwoza-Limankara a Jihar Borno.

“Yawancinsu tirsasa su a ka yi su ka shiga Boko Haram lokacin su na ƙanana.
“A yanzu haka sama da mayaƙan Boko Haram 17,000 ne su ka saduda duk da yunƙuri da ISWAP ke yi ta daƙile su daga miƙa kansu,” in ji jami’in tsaron.

Haka-zalika PRNigeria ta jiyo cewa dakarun Nijeriya na nan na fafatawa da mayaƙan ISWAP a daren Laraba a Malam Fatori.

Malam Fatori ya zama yankin da ISWAP ta fi ƙarfi inda har ta kafa ma majalisar shura a yankin wanda ya ke bida da Ƙasar Nijer.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp