fidelitybank

Mayaƙan Boko Haram sun ajiye makamai a Gwoza, yayin da dakarun Nijeriya su ka fafata da ISWAP a Malam Fatori

Date:

An samu ƙarin wasu mayaƙan Boko Haram sun miƙa kansu ga dakarun Nijeriya a jiya Laraba da safe, inda da yamma kuma dakarun Nijeriya su ka fafata da mayaƙan ISWAP a Malam Fatori.

Kwamndojin Boko Haram da ƴan barandansu ne dai su ka miƙa kansu da ajiye makamai ga dakarun gwamnatin Nijeriya, duk da ISWAP ta yi yunƙurin ta hana faruwar hakan.
Majiyar sirri ta sojojin Nijeriya ta baiyanawa PRNigeria cewa za a samu ƙarin ƴan Boko Haram da za su miƙa kansu zuwa ƙarshen shekara.

“Wasu daga cikin kwamndojin mayaƙan Boko Haram da ƴan barandansu sun tsere daga yankin Jaje a dajin Sambisa, in da tuni su ka miƙa kansu ga dakarun rundunar soji ta 192 da ke Gwoza-Limankara a Jihar Borno.

“Yawancinsu tirsasa su a ka yi su ka shiga Boko Haram lokacin su na ƙanana.
“A yanzu haka sama da mayaƙan Boko Haram 17,000 ne su ka saduda duk da yunƙuri da ISWAP ke yi ta daƙile su daga miƙa kansu,” in ji jami’in tsaron.

Haka-zalika PRNigeria ta jiyo cewa dakarun Nijeriya na nan na fafatawa da mayaƙan ISWAP a daren Laraba a Malam Fatori.

Malam Fatori ya zama yankin da ISWAP ta fi ƙarfi inda har ta kafa ma majalisar shura a yankin wanda ya ke bida da Ƙasar Nijer.

hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mun ceto tsohuwa ƴar shekaru 80 daga masu garkuwa – Ƴansanda

Rundunar ƴansandan jihar Jigawa, ta ce ta ceto wata...

APC na taron kasu ruwa da tsaki

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya za ta gudanar da...

Matatar Ɗangote ta sake karya farashin fetur

Kamfanin Dangote da ya mallaki matatar mai ta Dangote...

Idan Isra’ila ta kai mana hari Amurka ce – Iran

Ministan harkokin wajen ƙasar Iran ya ce, gwamnatin Tehran...

Kotu ta daure mai kiwon Akuya bayan ta cinye shukokin gwamnatin Kano

Wata kotun majistare da ke Kano ta daure wasu...

‘Yansanda sun dakile yi garkuwa da mutane a Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina ta dakile wani yunkurin...

‘Yansanda sun dakume ‘Yan Fashi uku a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu ‘yan...

Jarumar Nollywood ta zama sojan ruwar Amurka

Fitacciyar jarumar nan ta Najeriya Grace Bassey wacce a...

Na yi takaicin barin Ancelloti daga Real Madrid – Carvajal

Dan wasan baya na kungiyar kwallon kafa ta Real...

Mu na shirin yin kawancen jam’iyya – PDP

Majalisar dattawa ta jam'iyyar PDP, ta bayyana shirin jam'iyyar...

Ana zanga-zanga a Binuwai sakamakon harbe Dalibi dan shekara 23

Wata zanga-zanga ta barke a Makurdi, babban birnin jihar...

A na cigaba da farautar Fursunonin Osun da suka tsere

Hukumar gyaran hali ta Najeriya (NCoS) ta ce, ta...
X whatsapp