fidelitybank

Mayakan ISWAP sun kona mutane da ransu a Borno

Date:

A na fargabar cewa mutane da dama sun rasa rayukan su yayin da wasu su ka jikkata, sakamakon wani hari da mayakan Boko Haram su ka kai yankin karamar hukumar, Askira Uba da ke Jihar Borno.

Bayanai sun ce mayakan sun kutsa kauyen Kilangal, mahaifar mataimakin kakakin Majalisar Dokokin Jihar, Injiniya Abdullahi Musa da tsakar ranar Lahadi, inda su ka cinna wa gidaje wuta.

Majiyar rahoton ta ce wani jirgin yaki na dakarun sojin sama ya kai dauki kauyen sa’o’i biyu, bayan aukuwar lamarin, sai dai tuni aikin gama ya gama.

A cewar majiyar, mayakan sun ci karensu babu babbaka a yayin da babu wata tirjiya da su ka fuskanta, inda a ke zargin cewa, mutane da dama sun tsere cikin jeji yayin da kuma wasu masu karar kwana ta cimma su.

A watan Nuwamba ne mayakan kungiyar, ISWAP masu ikirarin jihadi a yammacin Afirka suka ka yi dauki ba dadi da dakarun sojin Najeriya a karamar hukumar, Askira Uba da ke Borno.

Aminiya ta rawaito cewa, mayakan sun yi wa Askira/Uba dirar mikiya ne da misalin karfe bakwai na safiya a cikin jerin gwanon motoci da su ka kai akalla 16, inda suka yi luguden wuta a yankin Ngude.

Wasu majiyoyi sun ce mazauna sun sanar da hukumomi game da shigowar mayakan amma ba a dauki mataki ba har suka fara bude wuta a yankin.

 

tribune news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka Æ´an Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation HaÉ—in-Kai sun ce sun kashe Æ´an...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aÆ™alla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naÉ—a shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp