A na fargabar cewa mutane da dama sun rasa rayukan su yayin da wasu su ka jikkata, sakamakon wani hari da mayakan Boko Haram su ka kai yankin karamar hukumar, Askira Uba da ke Jihar Borno.
Bayanai sun ce mayakan sun kutsa kauyen Kilangal, mahaifar mataimakin kakakin Majalisar Dokokin Jihar, Injiniya Abdullahi Musa da tsakar ranar Lahadi, inda su ka cinna wa gidaje wuta.
Majiyar rahoton ta ce wani jirgin yaki na dakarun sojin sama ya kai dauki kauyen sa’o’i biyu, bayan aukuwar lamarin, sai dai tuni aikin gama ya gama.
A cewar majiyar, mayakan sun ci karensu babu babbaka a yayin da babu wata tirjiya da su ka fuskanta, inda a ke zargin cewa, mutane da dama sun tsere cikin jeji yayin da kuma wasu masu karar kwana ta cimma su.
A watan Nuwamba ne mayakan kungiyar, ISWAP masu ikirarin jihadi a yammacin Afirka suka ka yi dauki ba dadi da dakarun sojin Najeriya a karamar hukumar, Askira Uba da ke Borno.
Aminiya ta rawaito cewa, mayakan sun yi wa Askira/Uba dirar mikiya ne da misalin karfe bakwai na safiya a cikin jerin gwanon motoci da su ka kai akalla 16, inda suka yi luguden wuta a yankin Ngude.
Wasu majiyoyi sun ce mazauna sun sanar da hukumomi game da shigowar mayakan amma ba a dauki mataki ba har suka fara bude wuta a yankin.