fidelitybank

Mayaƙan Boko Haram sun ajiye makamai a Gwoza, yayin da dakarun Nijeriya su ka fafata da ISWAP a Malam Fatori

Date:

An samu ƙarin wasu mayaƙan Boko Haram sun miƙa kansu ga dakarun Nijeriya a jiya Laraba da safe, inda da yamma kuma dakarun Nijeriya su ka fafata da mayaƙan ISWAP a Malam Fatori.

Kwamndojin Boko Haram da ƴan barandansu ne dai su ka miƙa kansu da ajiye makamai ga dakarun gwamnatin Nijeriya, duk da ISWAP ta yi yunƙurin ta hana faruwar hakan.
Majiyar sirri ta sojojin Nijeriya ta baiyanawa PRNigeria cewa za a samu ƙarin ƴan Boko Haram da za su miƙa kansu zuwa ƙarshen shekara.

“Wasu daga cikin kwamndojin mayaƙan Boko Haram da ƴan barandansu sun tsere daga yankin Jaje a dajin Sambisa, in da tuni su ka miƙa kansu ga dakarun rundunar soji ta 192 da ke Gwoza-Limankara a Jihar Borno.

“Yawancinsu tirsasa su a ka yi su ka shiga Boko Haram lokacin su na ƙanana.
“A yanzu haka sama da mayaƙan Boko Haram 17,000 ne su ka saduda duk da yunƙuri da ISWAP ke yi ta daƙile su daga miƙa kansu,” in ji jami’in tsaron.

Haka-zalika PRNigeria ta jiyo cewa dakarun Nijeriya na nan na fafatawa da mayaƙan ISWAP a daren Laraba a Malam Fatori.

Malam Fatori ya zama yankin da ISWAP ta fi ƙarfi inda har ta kafa ma majalisar shura a yankin wanda ya ke bida da Ƙasar Nijer.

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp