Wani matsafi mai suna, Alfa Tunde Olayiwola, wanda ke hannun ‘yan sanda a Akure da ke jihar Ondo bisa zargin mallakar wani kokon kan mutum ya fadi ya mutu a ranar Asabar.
Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan, DSP Olufunmilayo Odunlami, wanda ya tabbatar da mutuwar wanda a ke zargin a ranar Lahadin da ta gabata, ya musanta cewa ya na dukansa ko kuma gallaza masa har lahira.
Odunlami ya ce, wanda a ke zargin ya nuna bakon abu ne a yammacin ranar Asabar, inda a ka garzaya da shi asibiti inda daga baya a ka tabbatar da rasuwarsa.
“Ko a asibitin babu wani alamar cewa akwai wani duka a jikinsa; kuma ba a azabtar da shi ba.
“Ba za a iya azabtar da shi ba saboda gaskiyar abin da ke tattare da shi ya riga ya fito fili.
“Wadanda su ke wurin lokacin da a ka gabatar da Olayiwola a gaban manema labarai sun lura cewa ba a azabtar da shi ba,” inji Odunlami.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Ondo, Mista Oyeyemi Oyediran, ya gurfanar da Olayiwola a gaban manema labarai a ranar 23 ga watan Disamba a Akure tare da wasu mutane takwas da aka kama bisa laifuka daban-daban.
Oyediran ya bayyana haka ne cewa ana zargin Olayiwola da hannu wajen hada-hadar kudi kuma an kama shi ne a ranar 23 ga watan Disamba a Oka a cikin Garin Ondo.
“A ranar 23 ga watan Disamba da misalin karfe 9.20 na safe ‘yan sanda sun samu labarin cewa Alfa Tunde Olayiwola, na shirin karbar wani kaya da a ke zargin kokon kan mutum ne.
“Nan take ‘yan sanda suka dauki matakin, su ka kama malamin a Unguwar Ajagbale da ke Oka, cikin Garin Ondo.
“An samu wani sabon kokon kan mutum a hannun Olayiwola lokacin da a ka kama shi.