fidelitybank

Matsafi ya mutu a hannun ‘yan sanda

Date:

Wani matsafi mai suna, Alfa Tunde Olayiwola, wanda ke hannun ‘yan sanda a Akure da ke jihar Ondo bisa zargin mallakar wani kokon kan mutum ya fadi ya mutu a ranar Asabar.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan, DSP Olufunmilayo Odunlami, wanda ya tabbatar da mutuwar wanda a ke zargin a ranar Lahadin da ta gabata, ya musanta cewa ya na dukansa ko kuma gallaza masa har lahira.

Odunlami ya ce, wanda a ke zargin ya nuna bakon abu ne a yammacin ranar Asabar, inda a ka garzaya da shi asibiti inda daga baya a ka tabbatar da rasuwarsa.

“Ko a asibitin babu wani alamar cewa akwai wani duka a jikinsa; kuma ba a azabtar da shi ba.

“Ba za a iya azabtar da shi ba saboda gaskiyar abin da ke tattare da shi ya riga ya fito fili.

“Wadanda su ke wurin lokacin da a ka gabatar da Olayiwola a gaban manema labarai sun lura cewa ba a azabtar da shi ba,” inji Odunlami.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Ondo, Mista Oyeyemi Oyediran, ya gurfanar da Olayiwola a gaban manema labarai a ranar 23 ga watan Disamba a Akure tare da wasu mutane takwas da aka kama bisa laifuka daban-daban.

Oyediran ya bayyana haka ne cewa ana zargin Olayiwola da hannu wajen hada-hadar kudi kuma an kama shi ne a ranar 23 ga watan Disamba a Oka a cikin Garin Ondo.

“A ranar 23 ga watan Disamba da misalin karfe 9.20 na safe ‘yan sanda sun samu labarin cewa Alfa Tunde Olayiwola, na shirin karbar wani kaya da a ke zargin kokon kan mutum ne.

“Nan take ‘yan sanda suka dauki matakin, su ka kama malamin a Unguwar Ajagbale da ke Oka, cikin Garin Ondo.

“An samu wani sabon kokon kan mutum a hannun Olayiwola lokacin da a ka kama shi.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...
X whatsapp