fidelitybank

Matsafi ya mutu a hannun ‘yan sanda

Date:

Wani matsafi mai suna, Alfa Tunde Olayiwola, wanda ke hannun ‘yan sanda a Akure da ke jihar Ondo bisa zargin mallakar wani kokon kan mutum ya fadi ya mutu a ranar Asabar.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan, DSP Olufunmilayo Odunlami, wanda ya tabbatar da mutuwar wanda a ke zargin a ranar Lahadin da ta gabata, ya musanta cewa ya na dukansa ko kuma gallaza masa har lahira.

Odunlami ya ce, wanda a ke zargin ya nuna bakon abu ne a yammacin ranar Asabar, inda a ka garzaya da shi asibiti inda daga baya a ka tabbatar da rasuwarsa.

“Ko a asibitin babu wani alamar cewa akwai wani duka a jikinsa; kuma ba a azabtar da shi ba.

“Ba za a iya azabtar da shi ba saboda gaskiyar abin da ke tattare da shi ya riga ya fito fili.

“Wadanda su ke wurin lokacin da a ka gabatar da Olayiwola a gaban manema labarai sun lura cewa ba a azabtar da shi ba,” inji Odunlami.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Ondo, Mista Oyeyemi Oyediran, ya gurfanar da Olayiwola a gaban manema labarai a ranar 23 ga watan Disamba a Akure tare da wasu mutane takwas da aka kama bisa laifuka daban-daban.

Oyediran ya bayyana haka ne cewa ana zargin Olayiwola da hannu wajen hada-hadar kudi kuma an kama shi ne a ranar 23 ga watan Disamba a Oka a cikin Garin Ondo.

“A ranar 23 ga watan Disamba da misalin karfe 9.20 na safe ‘yan sanda sun samu labarin cewa Alfa Tunde Olayiwola, na shirin karbar wani kaya da a ke zargin kokon kan mutum ne.

“Nan take ‘yan sanda suka dauki matakin, su ka kama malamin a Unguwar Ajagbale da ke Oka, cikin Garin Ondo.

“An samu wani sabon kokon kan mutum a hannun Olayiwola lokacin da a ka kama shi.

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp