fidelitybank

Matsafi ya mutu a hannun ‘yan sanda

Date:

Wani matsafi mai suna, Alfa Tunde Olayiwola, wanda ke hannun ‘yan sanda a Akure da ke jihar Ondo bisa zargin mallakar wani kokon kan mutum ya fadi ya mutu a ranar Asabar.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan, DSP Olufunmilayo Odunlami, wanda ya tabbatar da mutuwar wanda a ke zargin a ranar Lahadin da ta gabata, ya musanta cewa ya na dukansa ko kuma gallaza masa har lahira.

Odunlami ya ce, wanda a ke zargin ya nuna bakon abu ne a yammacin ranar Asabar, inda a ka garzaya da shi asibiti inda daga baya a ka tabbatar da rasuwarsa.

“Ko a asibitin babu wani alamar cewa akwai wani duka a jikinsa; kuma ba a azabtar da shi ba.

“Ba za a iya azabtar da shi ba saboda gaskiyar abin da ke tattare da shi ya riga ya fito fili.

“Wadanda su ke wurin lokacin da a ka gabatar da Olayiwola a gaban manema labarai sun lura cewa ba a azabtar da shi ba,” inji Odunlami.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Ondo, Mista Oyeyemi Oyediran, ya gurfanar da Olayiwola a gaban manema labarai a ranar 23 ga watan Disamba a Akure tare da wasu mutane takwas da aka kama bisa laifuka daban-daban.

Oyediran ya bayyana haka ne cewa ana zargin Olayiwola da hannu wajen hada-hadar kudi kuma an kama shi ne a ranar 23 ga watan Disamba a Oka a cikin Garin Ondo.

“A ranar 23 ga watan Disamba da misalin karfe 9.20 na safe ‘yan sanda sun samu labarin cewa Alfa Tunde Olayiwola, na shirin karbar wani kaya da a ke zargin kokon kan mutum ne.

“Nan take ‘yan sanda suka dauki matakin, su ka kama malamin a Unguwar Ajagbale da ke Oka, cikin Garin Ondo.

“An samu wani sabon kokon kan mutum a hannun Olayiwola lokacin da a ka kama shi.

www.legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp