fidelitybank

Matashi ya yi garkuwa da yarinya ya kuma yanka ta a Kano

Date:

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta kama wani matashi da ya yi garkuwa da wata yarinya yar kimanin shekaru 13 da haihuwa, har sai da ya kashe ta saboda ya fahimci cewa yarinyar ta gane shi.

Mai magana da yawun rundunar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan ga manema labarai.

Ya ce”A ranar 21/06/2021 sun samu rahoto daga wani mazaunin garin Tofa da ke ƙaramar hukumar Tofa a jihar Kano, cewa an yi garkuwa da ‘yarsa mai suna Zuwaira mai shekaru 13 tare da buƙatar ya bayar da kuɗin fansa naira miliyan daya. Daga baya a ka koma Naira 400,000.00.

“Yayin da a ke tattaunawa domin neman kudin fansar, sai aka gano gawar yarinyar a wani kango inda aka yankata kuma aka binne a wajen.

”Bayan samun rahoton, an ziyarci wurin, a ka tono gawar, likitoci kuma suka tabbatar da mutuwar ta, inda muka mika gawar ga ’yan uwanta don a yi mata jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada”. Inji kiyawa

Sanarwa ta kuma ce hakan tasa kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Sama’ila Shu’aibu Dikko, ya umurci rundunar ‘Operation Puff Adder’ ƙarƙashin jagorancin SP Shehu Dahiru waɗanda Allah ya basu ikon kama wanda ake zargi da aikata laifin wato Auwalu Abdulrashid, wanda ake kira da Lauje, Dan kimanin shekaru 21 a ƙauyen Ɗan Marke kauyen Dan Marke.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp