Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta kama wani matashi da ya yi garkuwa da wata yarinya yar kimanin shekaru 13 da haihuwa, har sai da ya kashe ta saboda ya fahimci cewa yarinyar ta gane shi.
Mai magana da yawun rundunar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan ga manema labarai.
Ya ce”A ranar 21/06/2021 sun samu rahoto daga wani mazaunin garin Tofa da ke ƙaramar hukumar Tofa a jihar Kano, cewa an yi garkuwa da ‘yarsa mai suna Zuwaira mai shekaru 13 tare da buƙatar ya bayar da kuɗin fansa naira miliyan daya. Daga baya a ka koma Naira 400,000.00.
“Yayin da a ke tattaunawa domin neman kudin fansar, sai aka gano gawar yarinyar a wani kango inda aka yankata kuma aka binne a wajen.
”Bayan samun rahoton, an ziyarci wurin, a ka tono gawar, likitoci kuma suka tabbatar da mutuwar ta, inda muka mika gawar ga ’yan uwanta don a yi mata jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada”. Inji kiyawa
Sanarwa ta kuma ce hakan tasa kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Sama’ila Shu’aibu Dikko, ya umurci rundunar ‘Operation Puff Adder’ ƙarƙashin jagorancin SP Shehu Dahiru waɗanda Allah ya basu ikon kama wanda ake zargi da aikata laifin wato Auwalu Abdulrashid, wanda ake kira da Lauje, Dan kimanin shekaru 21 a ƙauyen Ɗan Marke kauyen Dan Marke.