fidelitybank

Matashi ya yi garkuwa da yarinya ya kuma yanka ta a Kano

Date:

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta kama wani matashi da ya yi garkuwa da wata yarinya yar kimanin shekaru 13 da haihuwa, har sai da ya kashe ta saboda ya fahimci cewa yarinyar ta gane shi.

Mai magana da yawun rundunar, DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan ga manema labarai.

Ya ce”A ranar 21/06/2021 sun samu rahoto daga wani mazaunin garin Tofa da ke ƙaramar hukumar Tofa a jihar Kano, cewa an yi garkuwa da ‘yarsa mai suna Zuwaira mai shekaru 13 tare da buƙatar ya bayar da kuɗin fansa naira miliyan daya. Daga baya a ka koma Naira 400,000.00.

“Yayin da a ke tattaunawa domin neman kudin fansar, sai aka gano gawar yarinyar a wani kango inda aka yankata kuma aka binne a wajen.

”Bayan samun rahoton, an ziyarci wurin, a ka tono gawar, likitoci kuma suka tabbatar da mutuwar ta, inda muka mika gawar ga ’yan uwanta don a yi mata jana’iza kamar yadda addinin Musulunci ya tanada”. Inji kiyawa

Sanarwa ta kuma ce hakan tasa kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Sama’ila Shu’aibu Dikko, ya umurci rundunar ‘Operation Puff Adder’ ƙarƙashin jagorancin SP Shehu Dahiru waɗanda Allah ya basu ikon kama wanda ake zargi da aikata laifin wato Auwalu Abdulrashid, wanda ake kira da Lauje, Dan kimanin shekaru 21 a ƙauyen Ɗan Marke kauyen Dan Marke.

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp