Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta yi holin wani mutum da ya yi garkuwa da kansa domin karbar kudin fansa a wurin mahaifin sa.
Mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis ga manema labarai.
Ya ce,”Sunan sa Hayatu Musa dan asalin garin Madobi a Kano, mahaifinsa ya kawo mana kara cewa masu garkuwa da mutane sun kama dansa tare da ya biya Naira Dubu Dari kudin fansa kafin a sake shi, bayan mun yi binciki mu ka gano kuma zancen ba haka bane”. A cewar SP Kiyawa.
Sai dai wanda a ke zargin mai suna Hayatu Musa ya tabbatar da cewa,”Ni da kai na ne na yi garkuwa da kai na babu wanda ya yi garkuwa, kuma na make murya ta, sannan na kirawo mahaifi na a waya na shaida masa halin da a ke ciki”.
A nasa jawabin mahaifin matashin ya ce,”Mun yi waya da masu garkuwa dama kudin da su ka bukata in ba su, a she da na ne da kansa ya makale murya ya kira ni domin ya karbi kudinsa”.
Daga baya dai sai da mahaifin sa ya biya kudin fansa Naira Dubu Saba’in a wajen mahaifin na sa, kamar yadda rundunar ta tabbatar da hakan.