fidelitybank

Matashi dan Jigawa ya rataye kansa a bishiya

Date:

Rundunan ‘yan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da wani mutum mai shekara 25 da ya kashe kansa ta hanyar rataya a wani gari da ke karamar hukumar Taura.

mai magana da yawun rundunar, ASP Lawan Shiisu Adam, wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin ya ce, mutumin wanda da farko aka bayar da rahoton batansa, an same shi ya rataye kansa ne a wata bishiya da ke bayan gari a kauyen Zangon Maje na karamar hukumar, inda ya yi amfani da wandonsa a matsayin igiya, a jiya Litinin, 24 ga watan Janairu, 2022.

Ya ce, a ranar Litinin ne Hakimin Kwalam, Alhaji Muttaka Uba ya kira su inda ya sheda musu cewa, wani mutum Naziru Badamasi, mai shekara 25 na kauyen Tsadawa da ke karamar hukumar Taura, wanda kuma ya ke da tabin hankali, ya bata bayan ya bar gida a ranar da misalin karfe goma sha biyu da rabi na rana.

ASP Shiisu ya ce, daga bisani ne aka gano mutumin ya rataye kansa a bayan garin kauyen Zangon Maje, wanda shi ma a yankin wannan karamar hukuma yake.

Kakakin ya ce, da samun wannan labari aka tura jami’an ‘yan-sanda suka je wurin, inda suka dauko gawar suka kai ta babban asibitin Ringim, inda likita ya tabbatar da cewa mutumin ya rasu.

Jami’in ya kara da cewa, daga baya ne suka mika wa ‘yan uwan mamacin gawar domin yi masa jana’iza kasancewar binciken farko-farko da suka yi ya nuna cewa ba wani zargi da ake na wata makarkashiya kan mutuwar.

vangurd 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mu na aiki tuÆ™uru wajen daÆ™ile ayyukan ta’adda a Najeriya – Christopher Musa

Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa...

Mayaƙan ISWAP sun harbe Manoma 23 a Borno

Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ISWAP ta kashe...

Real Madrid ta É—auki É—an wasan baya daga Bournemouth

Real Madrid ta sanar da sayen É—an wasan baya...

Gwamnatin Kano ta haramta yin bikin Ƙauyawa da gidajen biki

Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da...

An kashe Æ´an Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...
X whatsapp