Rundunan ‘yan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da wani mutum mai shekara 25 da ya kashe kansa ta hanyar rataya a wani gari da ke karamar hukumar Taura.
mai magana da yawun rundunar, ASP Lawan Shiisu Adam, wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin ya ce, mutumin wanda da farko aka bayar da rahoton batansa, an same shi ya rataye kansa ne a wata bishiya da ke bayan gari a kauyen Zangon Maje na karamar hukumar, inda ya yi amfani da wandonsa a matsayin igiya, a jiya Litinin, 24 ga watan Janairu, 2022.
Ya ce, a ranar Litinin ne Hakimin Kwalam, Alhaji Muttaka Uba ya kira su inda ya sheda musu cewa, wani mutum Naziru Badamasi, mai shekara 25 na kauyen Tsadawa da ke karamar hukumar Taura, wanda kuma ya ke da tabin hankali, ya bata bayan ya bar gida a ranar da misalin karfe goma sha biyu da rabi na rana.
ASP Shiisu ya ce, daga bisani ne aka gano mutumin ya rataye kansa a bayan garin kauyen Zangon Maje, wanda shi ma a yankin wannan karamar hukuma yake.
Kakakin ya ce, da samun wannan labari aka tura jami’an ‘yan-sanda suka je wurin, inda suka dauko gawar suka kai ta babban asibitin Ringim, inda likita ya tabbatar da cewa mutumin ya rasu.
Jami’in ya kara da cewa, daga baya ne suka mika wa ‘yan uwan mamacin gawar domin yi masa jana’iza kasancewar binciken farko-farko da suka yi ya nuna cewa ba wani zargi da ake na wata makarkashiya kan mutuwar.