fidelitybank

Matashi dan Jigawa ya rataye kansa a bishiya

Date:

Rundunan ‘yan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da wani mutum mai shekara 25 da ya kashe kansa ta hanyar rataya a wani gari da ke karamar hukumar Taura.

mai magana da yawun rundunar, ASP Lawan Shiisu Adam, wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin ya ce, mutumin wanda da farko aka bayar da rahoton batansa, an same shi ya rataye kansa ne a wata bishiya da ke bayan gari a kauyen Zangon Maje na karamar hukumar, inda ya yi amfani da wandonsa a matsayin igiya, a jiya Litinin, 24 ga watan Janairu, 2022.

Ya ce, a ranar Litinin ne Hakimin Kwalam, Alhaji Muttaka Uba ya kira su inda ya sheda musu cewa, wani mutum Naziru Badamasi, mai shekara 25 na kauyen Tsadawa da ke karamar hukumar Taura, wanda kuma ya ke da tabin hankali, ya bata bayan ya bar gida a ranar da misalin karfe goma sha biyu da rabi na rana.

ASP Shiisu ya ce, daga bisani ne aka gano mutumin ya rataye kansa a bayan garin kauyen Zangon Maje, wanda shi ma a yankin wannan karamar hukuma yake.

Kakakin ya ce, da samun wannan labari aka tura jami’an ‘yan-sanda suka je wurin, inda suka dauko gawar suka kai ta babban asibitin Ringim, inda likita ya tabbatar da cewa mutumin ya rasu.

Jami’in ya kara da cewa, daga baya ne suka mika wa ‘yan uwan mamacin gawar domin yi masa jana’iza kasancewar binciken farko-farko da suka yi ya nuna cewa ba wani zargi da ake na wata makarkashiya kan mutuwar.

vanguard new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp