Rundunar ‘yan sandan Jihar Kano, ta tabbatar da mutuwar wata mata da a ke zargin ta kashe kanta a unguwar Sheka da ke Ƙaramar Hukumar Kumbotso.
‘Yan sandan dai sun ce matar ta kashe kanta ne ta hanyar amfani da wani fasasshen gilashin taga na Luba, ta yanka kanta bayan gartsa wa mahaifinta cizo, sannan ta gutsire dan yatsanta da ke ciwo na Karkare.
Wani dan uwan marigayiyar mai suna, Muhammad Sanusi, ya ce“Kafin ‘yar uwar ta wa ta su ta kashe kanta ta yi fama da ciwon yatsa wato karkare, wanda har sai da ta kai ga mun rufe ta a ɗaki na tsawon kwana biyar, sakamakon yadda ta koma tamkar mai taɓin hankali, a ranar da mu ka buɗe ta ne ta fasa gilashin tagar ɗakin da a ka rufe ta sannan ta yanka kanta a makogoro”.
A shekarar 2021 an samu mutane sama da biyar da suka kashe kansu a Kano, wanda wasu daga cikinsu aka alaƙanta su da matsalar ƙwaƙwalwa.
Na baya-bayan da aka samu shi ne na wani matashi da ya kashe kan sa ta hanyar yanke al’aurar sa, a cewar BBC.