Masu zanga-zanga a Burkina Faso sun ƙona shelkwatar jam’iyya mai mulki a Burkina Faso ta MPP a Ouagadougou babban birnin ƙasar.
Rahotanni na nuni da cewa ‘yan sanda sun samu nasarar tarwatsa su da hayaƙi mai sa hawaye bayan sun far wa ginin.
Masu zanga-zangar sun ƙona tayoy, inda suke goyon bayan sojojin da ke yunƙurin juyin mulki da kuma neman manyan jami’an ƙasar da su sauka daga kan mulki.
Haka kuma masu zanga-zangar na neman a ƙara ƙaimi a yaƙin da ake yi da masu iƙirarin jihadi waɗanda ke ƙara zafafa hare-hare a ƙasar.
Masu zanga-zangar dai sun fito ne sa’o’i bayan da aka yi musayar wuta mai ƙarfi a wasu sansanonin sojoji a Ouagadougou da garuruwan da ke Arewacin ƙasar.
Gwamnatin ƙasar ta yi kira da a zauna lafiya, kuma ta musanta yunƙurin da ake yi na juyin mulki a ƙasar.