fidelitybank

Masu garkuwa sun saki shugaban ASUU da dan takarar gwamna

Date:

Masu garkuwa da mutane sun sako shugaban kungiyar malaman jami’o’i (ASUU), reshen jami’ar jihar Filato, Hassan Zitta, da tsohon dan takarar gwamna a jihar, Nicholas Nshe.

Sakataren kungiyar, Samson Deme ne ya tabbatar da hakan ga jaridar Premium ta wayar tarho.

Ya ce,”An sako mutanen biyu ne a daren ranar Talata bayan sun shafe kwanaki 11 a wurin masu garkuwa da mutane. Akalla an biya kudin fansa Naira miliyan 10 kafin a sako su.

Ya kuma ce, “Bayan an biya Naira miliyan 10 ba a sake su ba. Sai da suka kara wasu kudi domin a sake su, amma ban san nawa ba.” An samu labarin cewa masu garkuwan sun bukaci kimanin Naira miliyan 90 yayin da su ka bukaci Naira miliyan 50 ga tsohon dan takarar gwamnan da kuma Naira miliyan 40 ga shugaban ASUU domin a sako su”.

Ya zuwa yanzu dai ba a samu jin ta bakin Ubah Ogaba, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Filato ba.

Mutanen biyu sun shafe kwanaki 11 tare da wadanda suka sace su bayan an yi garkuwa da su a jajibirin sabuwar shekara a gidan tsohon dan takarar gwamna kuma tsohon shugaban karamar hukumar Shendam, Mista Nshe.

daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp