Masu garkuwa da mutane sun sako shugaban kungiyar malaman jami’o’i (ASUU), reshen jami’ar jihar Filato, Hassan Zitta, da tsohon dan takarar gwamna a jihar, Nicholas Nshe.
Sakataren kungiyar, Samson Deme ne ya tabbatar da hakan ga jaridar Premium ta wayar tarho.
Ya ce,”An sako mutanen biyu ne a daren ranar Talata bayan sun shafe kwanaki 11 a wurin masu garkuwa da mutane. Akalla an biya kudin fansa Naira miliyan 10 kafin a sako su.
Ya kuma ce, “Bayan an biya Naira miliyan 10 ba a sake su ba. Sai da suka kara wasu kudi domin a sake su, amma ban san nawa ba.” An samu labarin cewa masu garkuwan sun bukaci kimanin Naira miliyan 90 yayin da su ka bukaci Naira miliyan 50 ga tsohon dan takarar gwamnan da kuma Naira miliyan 40 ga shugaban ASUU domin a sako su”.
Ya zuwa yanzu dai ba a samu jin ta bakin Ubah Ogaba, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Filato ba.
Mutanen biyu sun shafe kwanaki 11 tare da wadanda suka sace su bayan an yi garkuwa da su a jajibirin sabuwar shekara a gidan tsohon dan takarar gwamna kuma tsohon shugaban karamar hukumar Shendam, Mista Nshe.