fidelitybank

Masu garkuwa sun saki shugaban ASUU da dan takarar gwamna

Date:

Masu garkuwa da mutane sun sako shugaban kungiyar malaman jami’o’i (ASUU), reshen jami’ar jihar Filato, Hassan Zitta, da tsohon dan takarar gwamna a jihar, Nicholas Nshe.

Sakataren kungiyar, Samson Deme ne ya tabbatar da hakan ga jaridar Premium ta wayar tarho.

Ya ce,”An sako mutanen biyu ne a daren ranar Talata bayan sun shafe kwanaki 11 a wurin masu garkuwa da mutane. Akalla an biya kudin fansa Naira miliyan 10 kafin a sako su.

Ya kuma ce, “Bayan an biya Naira miliyan 10 ba a sake su ba. Sai da suka kara wasu kudi domin a sake su, amma ban san nawa ba.” An samu labarin cewa masu garkuwan sun bukaci kimanin Naira miliyan 90 yayin da su ka bukaci Naira miliyan 50 ga tsohon dan takarar gwamnan da kuma Naira miliyan 40 ga shugaban ASUU domin a sako su”.

Ya zuwa yanzu dai ba a samu jin ta bakin Ubah Ogaba, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Filato ba.

Mutanen biyu sun shafe kwanaki 11 tare da wadanda suka sace su bayan an yi garkuwa da su a jajibirin sabuwar shekara a gidan tsohon dan takarar gwamna kuma tsohon shugaban karamar hukumar Shendam, Mista Nshe.

legitnews.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Turji ya saki Mutane 32 bayan zaman sulhu

Shahararren shugaban ‘yan bindiga, Bello Turji, ya saki mutane...

ADC ta gargadi El’Rufa’i kan ruguza jam’iyyar

Shugaban jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a jihar Kaduna,...

An gindayawa Thomas Partey sharudan beli

An gindaya sharuddan belin tsohon dan wasan tsakiya na...

Fursunoni 37 na jiran zartas musu da hukuncin kisa a Bauchi

Fursunoni 37 da aka yanke wa hukuncin kisa bisa...

Kwamitin sulhu na MDD zai gana kan makomar ƴan Isra’ila da ke hannun Hamas

Kwamitin tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya zai tattauna yau...

Sojoji sun kashe ‘yan Boko Haram 17 a Borno da Adamawa

Sojoji da ke aiki ƙarƙashin rundunar Operation Haɗin Kai...

Falana ya caccaki Tinubu kan salon tattalin arzikin Najeriya

Fitaccen lauyan nan mai kare haƙƙin bil adama, Femi...

Yahudawa sun yiwa Netanyahu tutsu kan mamaye Gaza

Ƴan'uwan Isra'ilawan da aka yi garkuwa da su a...

Cin zarafin Daliba ya sanya yin zanga-zanga a China

Zanga-zanga ta ɓarke a kudancin China sakamakon cin zarafin...

Tinubu ya baiwa ‘yan wasan kwallon kwando dala dubu 100 da filaye a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta karrama kungiyar kwallon kwando ta mata...

‘Yan siyasa na kara matsin lamba Jonathan ya fito takara a 2027 – Bashir

Tsohon mai taimaka wa tsohon shugaban kasa kan harkokin...

Gwamnati ta karbi tawagar ‘yan wasan kwallon kwando D’Tigress

Tawagar ƴan wasan ƙwallon kwando mata ta Najeriya ta...
X whatsapp