Ministan shari’a kuma babban lauyan gwamnatin tarayya, Abubakar Malami (SAN), ya ce yanzu haka an ayyana masu garkuwa da mutane a matsayin ‘yan ta’adda.
Ya ce sanarwar da kotun ta fitar na baya-bayan nan ya fito fili, kuma nan ba da jimawa ba za a wallafa. Ya kuma bayyana cewa an sanar da dukkan hukumomin tsaro da abin ya shafa.
Malami ya bayyana haka ne a lokacin da ya ke bayyana hakan a wani shirin Siyasa a Yau, wanda wakilin mu ya bibiyi shirin na gidan Talabijin na Channels daga Abuja ranar Laraba.
A ranar Alhamis din makon jiya ne wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta bayyana ‘yan bindiga a matsayin ‘yan ta’adda.