fidelitybank

Masarauci mafi daɗewa a masarautar Kano,  Sarkin Bai Adnan ya rasu

Date:

 

Sarkin Ban Kano, Tsohon Hakimin Ɗambatta, Dakta Mukhtar Adnan ya rasu.

Marigayi Adnan, ya rasu ya na da shekara 95 a wani asibiti da asubar yau Juma’a a Kano.

Kafin rasuwarsa, marigayin shine Kwamishinan Ilimi na farko a tarihin Kano.

Dakta Adnan ya kasance ɗan majalisar Sarki tun a shekarar 1954.

Marigayin ya kuma kasance ɗaya da ga cikin masu naɗin Sarki, inda da shi a ka naɗa Sarkin Kano, marigayi Alhaji Ado Bayero a 1963.

Tun a 1953 marigayi Adnan ya zama Hakimin Ɗambatta har zuwa shekarar 2019, inda a ka cire daga hakimcin sakamakon sabuwar dokar masarauta da Gwamna Abdullahi Ganduje ya ƙirkiro.

Wannan jarida ta jiyo cewa da safen nan ne dai za a yi jana’izar Sarkin Bai kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a sanar da lokacin da za a yi jana’izar marigayin ba.

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp