Manchester United ta nada Ralf Rangnick a matsayin kocinta na wucin gadi har zuwa karshen kakar wasa ta bana.
Mai horaswar mai shekaru 63 ya karbi aikin ne daga Ole Gunnar Solskjaer, wanda aka kora ranar 21 ga watan Nuwamba, bayan da Watford ta doke su da ci 4 da 1.
Rangnick ya bar aikinsa na shugaban wasanni da ci gaba a kungiyar Lokomotiv Moscow ta kasar Rasha domin fara aikin.
Rangnick ya ce “Na yi matukar farin ciki da komawa Manchester United kuma na mai da hankali kan ganin wannan kakar wasan ta samu nasara.”