fidelitybank

Man Fetur: Kungiyar Kwadago za ta tsunduma yajin aiki a sabuwar shekara

Date:

Kungiyar kwadago ta Najeriya NLC ta bayyana shirin fara shiga zanga-zanga a fadin kasar a ranar 27 ga watan Janairu na 2022, domin nuna adawa da matakin da gwamnatin Najeriya ta dauka na kara farashin man fetur.

Hakan na kunshe ne a cikin wata wasika da babban sakataren kungiyar, Kwamrade Emmanuel Ugboaja, ya aikewa shugabannin kungiyoyin a jihohi 36 na tarayya.

Wasikar ta bukaci shugabannin zartaswa da su kira taron majalisar zartarwa ta Jihohi (SEC) inda za su tsara dabarun tabbatar da nasarar aikin a jihohinsu.

A wani mataki kan kudurin cewa, za ta jagoranci zanga-zangar a Jihohi 36 na Tarayyar Najeriya a ranar 27 ga watan Janairu 2022, domin nuna adawa da shirin da gwamnatin tarayya ta yi na kara farashin man fetur’.

Sanarwar ta kuma ce,“Za ku iya tunawa cewa Majalisa ta gudanar da taron Majalisar Zartarwa ta Kasa (NEC) a ranar Juma’a, 17 ga Disamba, 2021, inda a ka dauki wasu muhimman shawarwari. A ci gaba da wadannan hukunce-hukuncen ne mu ka rubuta, domin sanar da ku cewa ranar 27 ga watan Janairu, 2022, mu ka tsayar a matsayin ranar da Majalisar za ta gudanar da zanga-zangar adawa da shirin gwamnatin tarayya na jihohi 36 na tarayya a kan kara farashin man fetur.

“An bukaci ku da ku kira taron majalisar zartarwa ta jiha (SEC) inda za ku tsara dabarun tabbatar da nasarar aikin a jihar ku. An kuma ba ku kwarin gwiwa da ku tuntubi abokan zamanmu na jama’a a jiharku a kokarin ku na gudanar da wannan gangamin”.

Tun da farko, wata gamayyar kungiyoyi masu rajin kafa Ma’aikata (Mass Workers Party) da kuma ‘yan Socialist Transformation of Nigeria, wato People’s Alternative Political Movement (TPAP-M), sun yi fatali da karin farashin iskar gas da kuma shirin da ke taf na. karin farashin man fetur da kudin wutar lantarki da dai sauransu.

Gamayyar kungiyoyin ta bayyana hakan ne a cikin sanarwar da ta fitar a taron jama’a da kungiyar TRAP-M da takwarorin ta su ka shirya kan karin farashin man fetur da wutar lantarki da ke gabatowa.

Ta ce za ta sake shirya wata zanga-zangar mamaya a Najeriya a bikin cika shekaru 10 na farko a watan Janairun 2022.

latest nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp