fidelitybank

Man Fetur: Kungiyar Kwadago za ta tsunduma yajin aiki a sabuwar shekara

Date:

Kungiyar kwadago ta Najeriya NLC ta bayyana shirin fara shiga zanga-zanga a fadin kasar a ranar 27 ga watan Janairu na 2022, domin nuna adawa da matakin da gwamnatin Najeriya ta dauka na kara farashin man fetur.

Hakan na kunshe ne a cikin wata wasika da babban sakataren kungiyar, Kwamrade Emmanuel Ugboaja, ya aikewa shugabannin kungiyoyin a jihohi 36 na tarayya.

Wasikar ta bukaci shugabannin zartaswa da su kira taron majalisar zartarwa ta Jihohi (SEC) inda za su tsara dabarun tabbatar da nasarar aikin a jihohinsu.

A wani mataki kan kudurin cewa, za ta jagoranci zanga-zangar a Jihohi 36 na Tarayyar Najeriya a ranar 27 ga watan Janairu 2022, domin nuna adawa da shirin da gwamnatin tarayya ta yi na kara farashin man fetur’.

Sanarwar ta kuma ce,“Za ku iya tunawa cewa Majalisa ta gudanar da taron Majalisar Zartarwa ta Kasa (NEC) a ranar Juma’a, 17 ga Disamba, 2021, inda a ka dauki wasu muhimman shawarwari. A ci gaba da wadannan hukunce-hukuncen ne mu ka rubuta, domin sanar da ku cewa ranar 27 ga watan Janairu, 2022, mu ka tsayar a matsayin ranar da Majalisar za ta gudanar da zanga-zangar adawa da shirin gwamnatin tarayya na jihohi 36 na tarayya a kan kara farashin man fetur.

“An bukaci ku da ku kira taron majalisar zartarwa ta jiha (SEC) inda za ku tsara dabarun tabbatar da nasarar aikin a jihar ku. An kuma ba ku kwarin gwiwa da ku tuntubi abokan zamanmu na jama’a a jiharku a kokarin ku na gudanar da wannan gangamin”.

Tun da farko, wata gamayyar kungiyoyi masu rajin kafa Ma’aikata (Mass Workers Party) da kuma ‘yan Socialist Transformation of Nigeria, wato People’s Alternative Political Movement (TPAP-M), sun yi fatali da karin farashin iskar gas da kuma shirin da ke taf na. karin farashin man fetur da kudin wutar lantarki da dai sauransu.

Gamayyar kungiyoyin ta bayyana hakan ne a cikin sanarwar da ta fitar a taron jama’a da kungiyar TRAP-M da takwarorin ta su ka shirya kan karin farashin man fetur da wutar lantarki da ke gabatowa.

Ta ce za ta sake shirya wata zanga-zangar mamaya a Najeriya a bikin cika shekaru 10 na farko a watan Janairun 2022.

dailysun

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp