Kungiyar kwadago ta Najeriya NLC ta bayyana shirin fara shiga zanga-zanga a fadin kasar a ranar 27 ga watan Janairu na 2022, domin nuna adawa da matakin da gwamnatin Najeriya ta dauka na kara farashin man fetur.
Hakan na kunshe ne a cikin wata wasika da babban sakataren kungiyar, Kwamrade Emmanuel Ugboaja, ya aikewa shugabannin kungiyoyin a jihohi 36 na tarayya.
Wasikar ta bukaci shugabannin zartaswa da su kira taron majalisar zartarwa ta Jihohi (SEC) inda za su tsara dabarun tabbatar da nasarar aikin a jihohinsu.
A wani mataki kan kudurin cewa, za ta jagoranci zanga-zangar a Jihohi 36 na Tarayyar Najeriya a ranar 27 ga watan Janairu 2022, domin nuna adawa da shirin da gwamnatin tarayya ta yi na kara farashin man fetur’.
Sanarwar ta kuma ce,“Za ku iya tunawa cewa Majalisa ta gudanar da taron Majalisar Zartarwa ta Kasa (NEC) a ranar Juma’a, 17 ga Disamba, 2021, inda a ka dauki wasu muhimman shawarwari. A ci gaba da wadannan hukunce-hukuncen ne mu ka rubuta, domin sanar da ku cewa ranar 27 ga watan Janairu, 2022, mu ka tsayar a matsayin ranar da Majalisar za ta gudanar da zanga-zangar adawa da shirin gwamnatin tarayya na jihohi 36 na tarayya a kan kara farashin man fetur.
“An bukaci ku da ku kira taron majalisar zartarwa ta jiha (SEC) inda za ku tsara dabarun tabbatar da nasarar aikin a jihar ku. An kuma ba ku kwarin gwiwa da ku tuntubi abokan zamanmu na jama’a a jiharku a kokarin ku na gudanar da wannan gangamin”.
Tun da farko, wata gamayyar kungiyoyi masu rajin kafa Ma’aikata (Mass Workers Party) da kuma ‘yan Socialist Transformation of Nigeria, wato People’s Alternative Political Movement (TPAP-M), sun yi fatali da karin farashin iskar gas da kuma shirin da ke taf na. karin farashin man fetur da kudin wutar lantarki da dai sauransu.
Gamayyar kungiyoyin ta bayyana hakan ne a cikin sanarwar da ta fitar a taron jama’a da kungiyar TRAP-M da takwarorin ta su ka shirya kan karin farashin man fetur da wutar lantarki da ke gabatowa.
Ta ce za ta sake shirya wata zanga-zangar mamaya a Najeriya a bikin cika shekaru 10 na farko a watan Janairun 2022.