fidelitybank

Malaman jami’o’i ku koma bakin aiki ko kuji a jikin ku – Gwamnatin Gombe

Date:

Hukumar gudanarwar ta jami’ar jihar Gombe, ta bukaci malaman jami’ar da su koma bakin aiki ko kuma ta dauki matakin nan na dakatar da albashin malaman da suka bijire.

Hukumar gudanarwar ta yanke wannan shawarar ne bayan wani zama da ta yi da kungiyar malaman, kana ta tsayar da ranar tara ga wannan watan na Satumba domin fara karatu gadan-gadan.

Mahukunta a jihar Gombe sun bayyana cewa duk wata kara da karamcin da ya kamata sun yi wa malaman jami’ar jihar a tsawon lokuta daban-daban da kungiyar malaman jami’a ta kasa ta kwashe mambobinta na yajin aiki, kasancewar gwamnatin jihar ba ta hana wa malaman ko da sisin kwabo ba, duk kuwa da cewa ba da ita suke fada ba.

Don haka ne ta nemi malaman jami`ar jihar da su fahince cewa tuwon girma miyarsa nama – kuma idan duniya da gaskiya to ya kamata a yi wa mazari riga da wando.

Bisa al`ada dai malaman da ke jami’o’i na jiha sukan yi biyayya ga uwar kungiyar ta kasa a duk lokacin da aka bukace su ko da kuwa matsalar ba ta shafe su kai-tsaye ba, kuma suna hakan ne saboda su gudu tare su tsira tare.

Kawo yanzu kungiyar malaman jami’ar jihar Gomben ba su ce uffan ba kan umarnin na gwamnati.

Sama da watanni 6 kenan da malaman jami`o`in gwamnatin Najeriya suka tsunduma yajin aiki, bayan wadanda suka yi a lokuta daban-daban da kulla yarjeniyoyi da dama tsakaninsu da gwamnati.

Sai dai har yanzu bangarorin biyu ba su daidaita ba, kuma dalibai ne ke shiga tsaka mai wuya kan yajin aikin.

vanguard news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta É—aure Matashin da ya shiga É—akin kwanan ÆŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp