Hukumar gudanarwar ta jami’ar jihar Gombe, ta bukaci malaman jami’ar da su koma bakin aiki ko kuma ta dauki matakin nan na dakatar da albashin malaman da suka bijire.
Hukumar gudanarwar ta yanke wannan shawarar ne bayan wani zama da ta yi da kungiyar malaman, kana ta tsayar da ranar tara ga wannan watan na Satumba domin fara karatu gadan-gadan.
Mahukunta a jihar Gombe sun bayyana cewa duk wata kara da karamcin da ya kamata sun yi wa malaman jami’ar jihar a tsawon lokuta daban-daban da kungiyar malaman jami’a ta kasa ta kwashe mambobinta na yajin aiki, kasancewar gwamnatin jihar ba ta hana wa malaman ko da sisin kwabo ba, duk kuwa da cewa ba da ita suke fada ba.
Don haka ne ta nemi malaman jami`ar jihar da su fahince cewa tuwon girma miyarsa nama – kuma idan duniya da gaskiya to ya kamata a yi wa mazari riga da wando.
Bisa al`ada dai malaman da ke jami’o’i na jiha sukan yi biyayya ga uwar kungiyar ta kasa a duk lokacin da aka bukace su ko da kuwa matsalar ba ta shafe su kai-tsaye ba, kuma suna hakan ne saboda su gudu tare su tsira tare.
Kawo yanzu kungiyar malaman jami’ar jihar Gomben ba su ce uffan ba kan umarnin na gwamnati.
Sama da watanni 6 kenan da malaman jami`o`in gwamnatin Najeriya suka tsunduma yajin aiki, bayan wadanda suka yi a lokuta daban-daban da kulla yarjeniyoyi da dama tsakaninsu da gwamnati.
Sai dai har yanzu bangarorin biyu ba su daidaita ba, kuma dalibai ne ke shiga tsaka mai wuya kan yajin aikin.