fidelitybank

Makamai: EU za ta kakabawa Myanmar sabon takunkumi

Date:

Kungiyar tarayyar Turai ta ce a shirye take ta kakaba wa kasar Myanmar karin takunkumi bayan wani sabon tashin hankalin da sojojin kasar su ka yi, sannan kuma ta bukaci da a kakabawa kasar takunkumin siyan makamai.

Hukumomin jin kai sun bayyana karara cewa  sama da mutane 30 da suka hada da mata da kananan yara ne sojoji suka kashe tare da kona gawarwakinsu a wani kauye da ke jihar Kayah da ke fama da rikici a kasar Myanmar a makon da ya gabata.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaitoo cewa, rundunar sojin Myanmar ta ce ta kashe wasu ‘yan ta’adda da makamai da ba a tantance adadinsu ba daga dakarun ‘yan adawa a wani kauye, bayan da su ka ki tsaya a shingin binciken sojojin, domin bincikar su..

A cikin wata sanarwa da babban jami’in kula da harkokin waje na kungiyar EU, Josep Borrell ya fitar a ranar Alhamis dinnan, ya ce “Saboda karuwar tashe-tashen hankula a Myanmar, a na bukatar kara daukar matakan kariya daga kasashen duniya, gami da sanya takunkumin makamai.”

Ya kara da cewa “EU kuma a shirye ta ke ta kara sanyawa gwamnatin soja takunkumi.”

Tun bayan juyin mulkin da sojoji su ka yi a watan Fabrairu, kungiyar EU ta kakaba wa sojojin Myanmar da shugabanninta da kuma hukumominta takunkumin karya tattalin arziki. Sannan EU ta  dakatar da taimakawa kasar ta fannin kudi.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp