Kungiyar tarayyar Turai ta ce a shirye take ta kakaba wa kasar Myanmar karin takunkumi bayan wani sabon tashin hankalin da sojojin kasar su ka yi, sannan kuma ta bukaci da a kakabawa kasar takunkumin siyan makamai.
Hukumomin jin kai sun bayyana karara cewa sama da mutane 30 da suka hada da mata da kananan yara ne sojoji suka kashe tare da kona gawarwakinsu a wani kauye da ke jihar Kayah da ke fama da rikici a kasar Myanmar a makon da ya gabata.
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaitoo cewa, rundunar sojin Myanmar ta ce ta kashe wasu ‘yan ta’adda da makamai da ba a tantance adadinsu ba daga dakarun ‘yan adawa a wani kauye, bayan da su ka ki tsaya a shingin binciken sojojin, domin bincikar su..
A cikin wata sanarwa da babban jami’in kula da harkokin waje na kungiyar EU, Josep Borrell ya fitar a ranar Alhamis dinnan, ya ce “Saboda karuwar tashe-tashen hankula a Myanmar, a na bukatar kara daukar matakan kariya daga kasashen duniya, gami da sanya takunkumin makamai.”
Ya kara da cewa “EU kuma a shirye ta ke ta kara sanyawa gwamnatin soja takunkumi.”
Tun bayan juyin mulkin da sojoji su ka yi a watan Fabrairu, kungiyar EU ta kakaba wa sojojin Myanmar da shugabanninta da kuma hukumominta takunkumin karya tattalin arziki. Sannan EU ta dakatar da taimakawa kasar ta fannin kudi.