fidelitybank

Makamai: EU za ta kakabawa Myanmar sabon takunkumi

Date:

Kungiyar tarayyar Turai ta ce a shirye take ta kakaba wa kasar Myanmar karin takunkumi bayan wani sabon tashin hankalin da sojojin kasar su ka yi, sannan kuma ta bukaci da a kakabawa kasar takunkumin siyan makamai.

Hukumomin jin kai sun bayyana karara cewa  sama da mutane 30 da suka hada da mata da kananan yara ne sojoji suka kashe tare da kona gawarwakinsu a wani kauye da ke jihar Kayah da ke fama da rikici a kasar Myanmar a makon da ya gabata.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaitoo cewa, rundunar sojin Myanmar ta ce ta kashe wasu ‘yan ta’adda da makamai da ba a tantance adadinsu ba daga dakarun ‘yan adawa a wani kauye, bayan da su ka ki tsaya a shingin binciken sojojin, domin bincikar su..

A cikin wata sanarwa da babban jami’in kula da harkokin waje na kungiyar EU, Josep Borrell ya fitar a ranar Alhamis dinnan, ya ce “Saboda karuwar tashe-tashen hankula a Myanmar, a na bukatar kara daukar matakan kariya daga kasashen duniya, gami da sanya takunkumin makamai.”

Ya kara da cewa “EU kuma a shirye ta ke ta kara sanyawa gwamnatin soja takunkumi.”

Tun bayan juyin mulkin da sojoji su ka yi a watan Fabrairu, kungiyar EU ta kakaba wa sojojin Myanmar da shugabanninta da kuma hukumominta takunkumin karya tattalin arziki. Sannan EU ta  dakatar da taimakawa kasar ta fannin kudi.

daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...

‘Yan Arewa su dakata da neman mulki har zuwa 2031 – Sakataren Gwamnati

Sakataren gwamnatin tarayya, SGF, George Akume, ya yi kira...

Matatar Dangote ta janye ƙarar da ta shigar kamfanin NNPCL a kotu

Matatar man Dangote ta janye ƙarar da ta shigar...

Ba mu baiwa Obi shawara ya janye daga takara ba – Kungiyar Inyamurai

Kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Worldwide,...

Dole ne APC ta bar mana kujerar mataimakin shugaban kasa – ANPP

Tsagin tsohuwar jam'iyyar All Nigeria Peoples Party wato ANPP...

Gwamna ya nada Sarkin Gusau

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da naɗin...

‘Yan Bindiga sun yi ikirarin kashe Daliban koyon aikin lauya a Benuwai

Ƴanbindiga da suka yi garkuwa da ɗaliban makarantar samun...

Tinubu ya gwangwaje tawagar Super Falcons da ruwan daloli da gidaje a Abuja

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bai wa ƴan wasan...

Super Falcons ta sauka a Abuja tare da yin zagayen nuna kofi

Tawagar Super Falcons ta Najeriya sun isa Abuja bayan...

Za a fuskanci katsewar wutar lantarki a Legas tsawon kwana 25

Masu amfani da wutar lantarki a jihar Legas na...

‘Yan Najeriya ku daina bayar da bayan katin dan kasar ku – NIMC

Hukumar Kula da shaidar ɗan ƙasa (NIMC), ta bayyana...

Likitoci a Legas sun fara yajin aiki saboda rage musu albashi

Ƙungiyar likitoci ta Legas (Medical Guild), wacce ke ƙarƙashin...
X whatsapp