fidelitybank

Majalisar na yunkurin raba ofishin Babban Mai Shari’a da na Ministan Shari’a

Date:

Majalisar Wakilai na duba yiwuwar amincewa da wata doka da za ta raba ofishin Antoni Janar na Tarayya daga ofishin Ministan Shari’a.

Haka kuma, idan aka amince da dokar, za a raba ofishin Antoni Janar na jiha daga ofishin Kwamishinan Shari’a.

Dokar, wacce ‘yan majalisar dokoki biyu daga jam’iyyar PDP suka hada kai wajen gabatarwa, Mansur Soro (Mazabar Darazo/Ganjuwa, Jihar Bauchi) da Oluwole Oke (Osun), tana samun goyon baya daga Kwamitin Gyaran Tsarin Mulki na Majalisar, wanda Mataimakin Kakakin Majalisar, Benjamin Kalu, ke shugabanta.

Dokar tana neman gyara Sashe na 150 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999 (wanda akaiwa gyara), ta hanyar ƙara sabon sakin layi na 1 da zai ce, “Za a sami Antoni Janar na Tarayya wanda zai kasance Babban Lauyan Tarayya kuma ba shi ne zai riƙe matsayin Ministan Shari’a ba. Shugaban kasa ne zai nada shi, bisa amincewar Majalisar Dattawa.”

Haka nan, dokar tana neman ƙara sabon sakin layi a Sashe na 195 na Tsarin Mulki. Sabon sakin layin da za a kara zai ce, “Za a sami Antoni Janar a kowace Jiha wanda zai kasance Babban Lauyan Jiha, Gwamna zai nada shi, bisa amincewar Majalisar Dokokin Jiha.”

Yayin da yake magana da yan jaridu kan manufar wannan doka, Soro ya ce, “Dalilin wannan mataki shi ne inganta kwarewa wajen gudanar da shari’ar laifuka, kare muradun jama’a, da kuma dakile amfani da tsarin shari’a wajen biyan bukatun siyasa a matakan tarayya da jihohi.”

A cewar dan majalisar, “Ministan Shari’a na Tarayya da Kwamishinonin Shari’a na Jihohi ana iya kwatanta su da masu ba da shawarar siyasa da ke bayar da shawarwari na shari’a ga majalisar ministoci da kuma lura da al’amuran manufofin shari’a.

“Antoni Janar, a gefe guda, yana jagorantar shari’o’i a madadin gwamnati, yana kula da gurfanarwa, da kuma bayar da shawarwari kan kudurorin doka da yarjejeniyoyi da gwamnati ke nazari.”

Ya lura cewa haɗakar ayyukan minista ko kwamishina da Antoni Janar na iya haifar da rikice-rikice da son rai, yana mai jaddada cewa dokar ta yi niyyar “kawar da rikici, rage hadarin shisshigi a siyasance, da kuma kara amintadda da tsarin shari’a a idon yan Najeriya”

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp