fidelitybank

Majalisar na yunkurin raba ofishin Babban Mai Shari’a da na Ministan Shari’a

Date:

Majalisar Wakilai na duba yiwuwar amincewa da wata doka da za ta raba ofishin Antoni Janar na Tarayya daga ofishin Ministan Shari’a.

Haka kuma, idan aka amince da dokar, za a raba ofishin Antoni Janar na jiha daga ofishin Kwamishinan Shari’a.

Dokar, wacce ‘yan majalisar dokoki biyu daga jam’iyyar PDP suka hada kai wajen gabatarwa, Mansur Soro (Mazabar Darazo/Ganjuwa, Jihar Bauchi) da Oluwole Oke (Osun), tana samun goyon baya daga Kwamitin Gyaran Tsarin Mulki na Majalisar, wanda Mataimakin Kakakin Majalisar, Benjamin Kalu, ke shugabanta.

Dokar tana neman gyara Sashe na 150 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999 (wanda akaiwa gyara), ta hanyar ƙara sabon sakin layi na 1 da zai ce, “Za a sami Antoni Janar na Tarayya wanda zai kasance Babban Lauyan Tarayya kuma ba shi ne zai riƙe matsayin Ministan Shari’a ba. Shugaban kasa ne zai nada shi, bisa amincewar Majalisar Dattawa.”

Haka nan, dokar tana neman ƙara sabon sakin layi a Sashe na 195 na Tsarin Mulki. Sabon sakin layin da za a kara zai ce, “Za a sami Antoni Janar a kowace Jiha wanda zai kasance Babban Lauyan Jiha, Gwamna zai nada shi, bisa amincewar Majalisar Dokokin Jiha.”

Yayin da yake magana da yan jaridu kan manufar wannan doka, Soro ya ce, “Dalilin wannan mataki shi ne inganta kwarewa wajen gudanar da shari’ar laifuka, kare muradun jama’a, da kuma dakile amfani da tsarin shari’a wajen biyan bukatun siyasa a matakan tarayya da jihohi.”

A cewar dan majalisar, “Ministan Shari’a na Tarayya da Kwamishinonin Shari’a na Jihohi ana iya kwatanta su da masu ba da shawarar siyasa da ke bayar da shawarwari na shari’a ga majalisar ministoci da kuma lura da al’amuran manufofin shari’a.

“Antoni Janar, a gefe guda, yana jagorantar shari’o’i a madadin gwamnati, yana kula da gurfanarwa, da kuma bayar da shawarwari kan kudurorin doka da yarjejeniyoyi da gwamnati ke nazari.”

Ya lura cewa haɗakar ayyukan minista ko kwamishina da Antoni Janar na iya haifar da rikice-rikice da son rai, yana mai jaddada cewa dokar ta yi niyyar “kawar da rikici, rage hadarin shisshigi a siyasance, da kuma kara amintadda da tsarin shari’a a idon yan Najeriya”

nigeria daily post

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp