Sakataren Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres, ya nemi shugabannin Taliban da su bar yara mata su ci gaba da zuwa makarantu domin neman ilimi a fadin Afghanistan.
Cikin wani sako da ya aike a jiya Talata, yayin bikin ranar Ilimi ta duniya, Sakataren MDD ya nemi yara su ci gaba da zuwa sakandire da jami’o’i domin ci gaban Æ™asar.
Ya Æ™ara da cewa, ” bayar da damar neman ilimi wani É“angare ne na ‘yan cin É—an adam, kuma wata dama ce ta haɓɓa girman al’umma da tattalin arziki da kuma samar wa daidaikun mutane aikin yi.”
MDD dai ba ta kallon gwamnatin Taliban a Afghanistan a matsayin halastacciya.
Mista Guterres ya yi kira ga duniya ta gyara tsarin ilimi domin samar da al’ummar da kowa ke da dama iri guda, a kuma samar da yanayin tattalin arziki da zai yi daidai da yanayin da ake ciki a kowacce kasa domin ci gaban duk wani dalibi a duniya.