Majalisar wakilan Najeriya ta ce, za ta kaddamar da bincike kan yawan man da ake amfani da shi da kuma halin da matatun man kasar ke ciki.
‘Yan majalisar sun bayyana hakan ne bayan da gwamnatin kasar ta ce, za ta ci gaba da bayar da tallafin man, inda Ministar kudi Zainab Ahmed ta ce, “Akwai bukatar a kara kasafin kudin kasar na wannan shekara da Naira tiriliyan 2.557 a matsayin kudin da za a biya tallafin”.
A jiya Laraba Ministar da ta bayyana hakan ta ce, kamfanin mai na kasar, NNPC, ne ya bukaci a ba shi Naira biliyan dubu uku, wato tiriliyan uku domin biyan tallafin man a wannan shekara ta 2022, wanda kiyasi ke nuna cewa a duk wata za a biya naira biliyan 270 a tallafin.
Wannan dai na zuwa ne bayan da gwamnatin kasar ta dakatar da shirinta na janye tallafin man daga watan Yuli kamar yadda ta tsara a baya.